Babban Labari

SSS ta mamaye CBN, ta karbe ikon ofishin Emefiele

SSS ta mamaye CBN, ta karbe ikon ofishin Emefiele

Daga WAKILINMU A ranar Litinin jami'an hukumar tsaro ta SSS suka mamaye ginin hedkwatar Babban Bankin Nijeriya (CBN) da ke Abuja inda suka karɓe ikon ofishin Gwamnan Bankin, Godwin Emefiele. Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewar ba yau SSS ta fara farautar Emefiele ba kan zargin almundahana. A baya, hukumar SSS ta buƙaci kotu ta ba ta izinin tsare Emefiele amma ya zamana ba ya ƙasa sakamakon hutu da ya tafi wanda zai ƙare ranar Talata, 17 ga Janairu. Sai dai a Disamban da ya gabata Babbar Kotun Abuja ta haramta wa SSS cafke Emefiele, ko tsare shi, ko kuma…
Read More
Rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani a Ondo

Rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani a Ondo

*An rasa ran mutum*Gwamnatin jihar ta saka dokar ta-ɓaci Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mutum ɗaya ya rasa ransa tare da lalata kadarori da dama sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin wasu Fulani da Hausawa mazauna yankin Ogbese da ke Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa a jihar Ondo. An tattaro cewa, rikicin da ya faro tun a yammacin ranar Talata 3 ga watan Junairun 2022 inda ya yi ƙamari da safiyar Laraba 4 ga watan Junairun 2022, wanda aka qona shaguna da dama na ’yan Arewa a babbar kasuwar garin. Har yanzu dai ba a san ainihin musabbabin faɗan a hukumance…
Read More
Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023

Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023 na Naira tiriliyan 21.83. Rattaɓa hannun ya haɗa da na ƙarin kasafin 2022 da Majalisar Tarayya ta sahale wa Buharin. Wannan dai shi ne karo na takwas kuma na ƙarshe da Buhari zai rattaɓa wa Kasafin Ƙasa hannu tun bayan da mulkin ƙasa ya koma hannunsa kusan shekara takwas da suka gabata. Da yake jawabi, Buhari ya ce an samu ƙarin tiriliyan N1.32 kan tiriliyan N20.51 da aka kasafta tun farko wanda hakan ya sa kasafin ya ƙaru zuwa tiriliyan N21.83. Shugaban ya ce…
Read More
2023: Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

2023: Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya taya 'yan Nijeriya murnar shiga sabuwar shekara ta 2023. Cikin saƙon nasa Buhari ya gode wa Allah da Ya ƙaddari 'yan ƙasar da ke raye ganin wannan lokaci. Ya yi fatan duka 'yan Nijeriya da suka kwanta dama kafin sabuwar shekarar, mutuwa ta zama hutu a gare su. Ya ce nan da wata biyar Nijeriya za ta samu sabon Shugaban Ƙasa da gwamnoni da sauransu. Don haka ya sha alwashin gudanar da sahihin zaɓe ƙarƙashin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), don bai wa 'yan ƙasa damar zaɓen shugabannin da suka dace. Ya…
Read More
Majalisa ta amince wa Buhari ƙarin kasafin biliyan N819

Majalisa ta amince wa Buhari ƙarin kasafin biliyan N819

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta amince da ƙarin kasafin biliyan N819 da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya gabatar mata don cike giɓin kasafin 2022. wannan na zuwa ne bayan da Majalisar ta ƙara wa'adin aiwatar da kasafin na 2022 zuwa ranar 31 ga Maris, 2023. Da farko dai Majalisar ta amince da tiriliyan N17.12 a matsayin kasafin 2022, daga bisani ta ƙara kasafin zuwa tiriliyan N17.31 bayan da Shugaba Buhari ya buƙaci hakan inda ya ce tasirin yaƙin Ukraine da Rasha ga tattalin arzikin ƙasa ya haifar da buƙatar ƙarin. A ranar Laraba Majlisar ta amince da kasafin bayan…
Read More
Wahalar fetur: Barazana ga bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara

Wahalar fetur: Barazana ga bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara

*Duk da gargaɗin DSS ƙarancin fetur na gurgunta harkokin rayuwa*’Yan Nijeriya sun koka da tsadar abinci da sufuri*Mun samar da miliyoyin ayyuka a fannin noma – Buhari Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu wahalar samun man fetur a Nijeriya cikin ’yan kwanakin nan yana matuƙar barazana ga samun walwala da jin daɗin al’ummar ƙasar a lokacin da suke ƙoƙarin gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara mai kamawa ta 2023. A ranakun Lahadi da Litinin, 25 da 26 ga Disamba, 2022, za a gudanar da bikin ranar Kirsimeti, sannan kuma a ranar wata Lahadin ce za ta kasance…
Read More
Buhari ya kinkimo bashin tiriliyan N3 duk da tiriliyan N45 da ake bin gwamnatinsa

Buhari ya kinkimo bashin tiriliyan N3 duk da tiriliyan N45 da ake bin gwamnatinsa

Gwamnatin Nijeriya ƙarƙashin jagorancin Muhammadu Buhari ta sake kinkimo bashin Dalar Amurka biliyan $9 daidai da Naira tiriliyan 3.98 daga Bankin Duniya. Daraktan Bankin Duniya a Nijeriya, Shubham Chaudhuri ne ya bayyana haka a wajen taron da ya shirya a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata. Shubham Chaudhuri ya ce, zaman Bankin Duniya a Nijeriya ba shi da burin da ya wuci taimaka wa ƙasar ficewa daga ƙangin talaucin da take ciki da kuma inganta rayuwar al'ummarta. A baya, jaridar Intel Region ta rawaito cewar, bashin da ake bin Nijeriya ya ƙaru zuwa Naira tiriliyan N45.8 ($103 billion) a…
Read More
Ɓatanci: Ganduje ya samu damar rataye Abduljabbar Kabara

Ɓatanci: Ganduje ya samu damar rataye Abduljabbar Kabara

*A gaggauta kashe ni, inji malamin*Yadda kotu ta yanke masa hukuncin kisa*An haramta karantawa ko sauraron wa’azinsa Daga BABANGIDA S GORA a Kano A ranar Alhamis ta jiya ne wata Babbar Kotun Shari'ar Musulunci da ta ke Ƙofar Kudu a cikin birnin Kano ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Ibrahim Sarki Yola ta bai wa Gamnan Jihar Kano izinin kashe Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ta hanyar rataya, wanda ta samu da hannu dumu-dumu kan furta kalaman ɓatanci ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammadu (SAW) bayan kimanin shekara ɗaya da watanni biyar da gurfanar da shi a gabanta. Malam Abduljabbar, wanda kotun ta same…
Read More
Ɓatanci: Kotu ta yanke wa Abduljabbar hukuncin kisa

Ɓatanci: Kotu ta yanke wa Abduljabbar hukuncin kisa

Daga WAKILINMU Kotun Shari'a a Kano ta yanke wa Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara hukuncin kisa ta hanyar rataya. Kotu ta yanke wa malamin hukuncin kisa ne bayan da ta same shi da laifin ɓatanci ga Annabi Muhammad (SAW). Da yake yanke hukuncin, Alƙalin Kotun ya kuma buƙaci Gwamnatin Kano ta ƙwace masallatai guda biyun da ke ƙarƙashin kulawar Abduljabbar. Kazalika, Alƙalin ya yi kira da a daina sanya karatuttukan Abduljabbar ɗin a ɗaukacin kafafen yaɗa labarai, haka ma hotunansa. Bayan haka, kotun ta bai wa malamin wa'adin kwana 30 a kan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin da aka yanke masa…
Read More
Gwamna Buni ya bayar da umurnin raba wa tsangayoyi 475 kayan abinci da tufafi a Yobe

Gwamna Buni ya bayar da umurnin raba wa tsangayoyi 475 kayan abinci da tufafi a Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu A ƙoƙarin sa na inganta rayuwar al'ummar jihar, Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya bai wa hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, umurnin raba wa makarantun tsangaya 475, wanda ake sa ran alarammomi da almajiransu 8,000 za su ci gajiyar tallafin kayan abinci da na masarufi haɗi da dilolin tufafin sakawa, barguna, tabarmin leda, bokitan ruwa da sauran su a faɗin jihar Yobe. Da take ƙaddamar da rabon tallafin a Tsangayar Slaramma Goni Yahaya dake unguwar Gwange a Damaturu, Sakataren Hukumar SEMA, Dr. Muhammad Goje, wanda Daraktan hukumar, Alhaji Hassan Bomai ya…
Read More