06
Nov
Daga BASHIR ISAH Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana a ranar Juma'ar da ta gabata cewa, ƙasar Faransa za ta maido wa Nijeriya kuɗi har Dala miliyan 150 wanda tsohon Shgugaban Ƙasa marigayi Janar Sani Abacha ya wawushe a halin rayuwarsa. Cikin sanarwar da ya fitar, mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya yaba wa Faransa da matakin maido da kuɗin da ta ɗauka. Da yake karɓar baƙuncin Ministar Harkokin Wajen Faransa, Catherine Colonna, Shugaba Tinubu ya yaba da kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Nijeriya da Faransa, yana mai cewa, fahimtar juna da ke…
