Babban Labari

Buhari zai ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewacin Nijeriya

Buhari zai ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewacin Nijeriya

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata ake sa ran Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewa wanda zai gudana a jihohin Bauchi da Gombe. Aikin wanda zai gudana a yankin Kolmani shi ne irinsa na farko da Arewacin Nijerya ya taɓa gani. Kimanin shekaru biyu da suka gabata aka gano arzikin man da ke kwance a yankin. Duk da dai irin wannan aiki ba shi ne farau ba a Kudancin ƙasar, amma wannan shi zai zama karon farko Arewa bayan da matsalar tsaro ta hana aiwatar da makamacin aikin a yankin Borno. Tun a 2016…
Read More
Canjin kuɗi: Majalisar Dattawa da EFCC sun bayyana matsayarsu

Canjin kuɗi: Majalisar Dattawa da EFCC sun bayyana matsayarsu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Dattawan Nijeriya ta ce, wa'adin ranar Talata 31 ga Junairu, 2023 da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayar na canja dukkan tsoffin kuɗaɗe zuwa sabbi a bankuna, ya yi kaɗan. Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da majalisar ta yi alƙawarin bayar da goyon bayan majalisa ga manufar CBN na sake fasalin Naira. Ƙudurin majalisar ya biyo bayan ƙudirin da Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Harkokin Banki, Inshora da sauran Cibiyoyin Hada-hadar Kuɗi, Sanata Sani Uba ya gabatar a ranar Laraba 16 ga watan Nuwamba, 2022. Majalisar Dattijai ta yi kira ga babban…
Read More
Rikicin gwamnati da ASUU na neman ƙara rincaɓewa

Rikicin gwamnati da ASUU na neman ƙara rincaɓewa

*An ɗage zana jarrabawa a Kano*”’Yan takarar Shugaban Ƙasa biyu na shirin cefanar da jami’o’I” Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta dage cewa ba za a biya malaman jami'o'i albashin aikin da ba su yi ba, daidai da manufar ‘ba aiki, ba albashi’. Ministan Ilimi, Adamu Adamu ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Abuja, ranar Laraba, 16 ga Nuwamba, 2022. Idan za a iya tunawa, a ranar Juma’a 16 ga watan Oktoba, 2022, ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta shafe watanni 8 tana yi,…
Read More
‘Yan siyasa na shirin ganin bayan shirin sauya fasalin takardun Naira

‘Yan siyasa na shirin ganin bayan shirin sauya fasalin takardun Naira

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan siyasar ƙasar nan da ke da biliyoyin Naira ɓoye a wajen banki sun yi yunƙurin hana ruwan shirin Babban Bankin Nijeriya (CBN) na neman sauya wa Naira fasali gudu. Rahotanni sun ce 'yan siyasar sun ƙi kai kuɗaɗen nasu banki ajiya domin yin amfani da su wajen harkokin zaɓen 2023. Jaridar ThisDay ta ranar Lahadi ta rawaito cewa, 'yan siyasar da lamarin ya shafa sun nemi Majalisar Ƙasa ta taka wa shirin sauya wa Nairar fasali burki gudun kada ya shafi maƙudan kuɗin da suka killace a waurare daban-daban sabanin banki don amfanin zaɓen 2023.…
Read More
Canja fasalin Naira: ’Yan ta’adda sun fara karɓar kuɗin Nijar

Canja fasalin Naira: ’Yan ta’adda sun fara karɓar kuɗin Nijar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar ta’addancin ISWAP, ta haramta karɓar Naira daga hannun manoma da sauran jama'a, biyo bayan matakin da Gwamnatin Nijeriya ta ɗauka na canja fasali takardun kuɗin ƙasar. Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ne dai Gwamnatin Nojeriya ta sanar da cewa ta yanke shawarar canja fasalin takardu na Naira 200 da 500 da kuma 1000, waɗanda za ta fara fitar da su nan da watan Disamba, sannan a ranar 31 ga Janairun 2023, za a daina karɓar tsoffin takardun. Sai dai bayanai na nuna cewa wannan mataki ya jefa mayaƙan ISWAP a yankin Tumbus…
Read More
2023: Gobe INEC za ta fara bajekolin rajistar zaɓe

2023: Gobe INEC za ta fara bajekolin rajistar zaɓe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta ce, za a fara bajekolin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a gobe Asabar. Festus Okoye, Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Kaɗa Ƙuri’a na Hukumar, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya a jiya Alhamis. Ya bayyana cewa, a taronta na mako-mako da aka gudanar a ranar Alhamis 10 ga Nuwamba, 2022, hukumar ta tattauna akan nuna gabaɗaya rajistar masu kaɗa ƙuri’a na ƙasa bakiɗaya, don sauraron ƙorafe-ƙorafe…
Read More
Da sanina CBN zai sauya tsarin Naira – Buhari

Da sanina CBN zai sauya tsarin Naira – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce da saninsa Babban Bankin Nijeriya (CBN) zai canza tsarin wasu takardun Naira. Buhari ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da 'yan jarida Halilu Ahmed Getso da Kamaluddeen Sani Shawai suka yi da shi a ranar Lahadi a Abuja. Da yake amsa tambayoyi, Buhari ya ce ya gamsu kuma yana da yaƙinin ƙasa za ta amfana da sauyin tsarin kuɗin da CBN ya ƙudiri aniyar aiwatarwa. Ya ce dalilan da CBN ya gabatar masa dangane da sauyin tsarin kuɗin, sun gamsar da shi cewa, lallai tattalin arzikin ƙasa zai amfana da…
Read More
Ba ni na kashe Ummita ba, inji ɗan Chana a gaban kotu

Ba ni na kashe Ummita ba, inji ɗan Chana a gaban kotu

Daga AMINA YUSUF ALI Mutumin nan ɗan asalin ƙasar Chana mai suna Geng Quangrong ya musanta zargin kashe budurwarsa mai suna Ummita da ake yi masa a gaban Babbar Kotun Kano.  An gurfanar da Geng Quarong a gaban wata kotu wacce take zamanta a kan titin Miller Road dake jihar Kano. Inda Geng wanda aka kama dumu-dumu yana yi wa budurwarsa Ummukulsum Sani Buhari, wadda aka fi sani da Ummita, yankan rago ya ƙeƙasa ƙasa ya ƙi amsar laifinsa.  A ranar 27 ga watan Oktoba, 2022 ne yayin zaman kotu ne dai Alƙalin kotun mai suna, Mai Shari'a Sunusi Ado…
Read More
2023: Na yafe wa Osinbajo, inji Tinubu

2023: Na yafe wa Osinbajo, inji Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan takarar kujerar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya ce, ba shi da sauran damuwa a ransa game da Mataimakin Shugaban Nijeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, yana mai cewa, ya yafe masa bisa takara da ya yi da shi a lokacin zaven fitar da gwani na jam’iyyar. Tsohon gwamnan na jihar Legas ya bayyana haka ne ranar Litinin lokacin da yake jawabi ga wata ƙungiyar da ta yi wa Osinbajo hidimar takarar shugaban ƙasa a Kano jawabi. A cigaba da fafatawa a zaɓen fidda gwanin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, an…
Read More
Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

*Jihohi huɗu a Kudu da iyakar Nijar na da hatsarin gaske*Ba haka ba ne, inji Gwamnatin Tarayya*Jami’an Amurka sun kai samame rukunin gidaje a Abuja*An kulle katafaren ginin ‘Jabi Mall’ a Abuja Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu husuma da jayayya sun ɓarke tsakanin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ofisoshin jakadancin Amurka da Ingila bisa zargin yiwuwar barazanar tsaro a Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja, da wasu jihohin ƙasar, inda yayin da ofisoshin jakadancin ke iqirarin tabbatar da barazanar, ita kuwa Gwamnatin Tarayya ƙaryatawa ta ke yi. Alhamis da ta gabata Ofishin Hulɗa da Ƙasashen Waje, Ƙasashe Rainon…
Read More