Babban Labari

Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

*An kasa samun matsaya kan ministocin Kano, Zamfara da Kebbi Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ƙarshe dai Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunayen mutane 28 da ya zaɓa a matsayin ministoci, domin naɗa su a matsayin mabobin Majalizar Zartarwar Tarayyar Nijeriya. Bayan an daɗe ana jiran jerin sunayen ne a jiya Alhamis Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya zo zauren majalisar da ƙarfe 12:05 na rana, inda bayan an yi addu’ar buɗe zaman zauren sai kuma ya bayyana cewa, majalisar za ta shiga wani zama na musamman. Bayan zaman ne ya fito ya bayyana jerin sunayen…
Read More
Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Daga BASHIR ISAH Sojoji a ƙasar Nijar sun yi wa Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum, juyin mulki ranar Laraba da daddare sa'o'i bayan da masu tsaronsa suka tsare shi a fadarsa. A jawabin da ya yi wa 'yan ƙasa kai tsaye a tashar talabijin ta ƙasar, Colonel-Major Amadou Abdramane ya bayyana cewa, “sojoji da sauran hukumomin tsaro sun yanke shawarar jawo ƙarshen gwamnatin da kuka sani. “Wannan ya biyo bayan ci gaba da taɓarɓarewar tsaron ƙasar da kuma rashin walwala da ingancin tattalin arziki," in ji shi. Sojojin sun ce an rufe iyakokin ƙsar, sannan an kafa dokar hana zirga-zirga a…
Read More
Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Daga BASHIR ISAH Shugaban Nijeriya kuma Shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), Bola Ahmed Tinubu, ya yi gargaɗin cewa ECOWAS ba za ta yarda da duk wani al'amari da zai haifar da cikas ga zaɓaɓɓiyar gwamnati a yammacin Afirka ba. Tinubu ya yi wannan gargaɗi ne a matsayin martani kan fargabar yiwuwar juyin mulki a Jamhuriyar Nijar inda sojojin ƙasar suka tsare Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum. Ya yi gargaɗin ne a matsayinsa na shugaban ECOWAS, cikin sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, inda ya bayyana datse fadar shugaban ƙasar Nijar da sojojin suka yi a matsayin…
Read More
Yau take sabuwar shekarar Musulunci, 1445

Yau take sabuwar shekarar Musulunci, 1445

Daga BASHIR ISAH A wannan Larabar aka shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1445. A ranar Talata Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana Laraba, 19 ga Yulin 2023 a matsayin 1 ga watan Muharram na sabuwar shekarar ta 1445H. Kafin wannan lokaci, Basaraken ya buƙaci al’ummar Musulmi da su nemi jinjirin watan Muharram a ranar Litinin da ta gabata. Watan Muharram shi ne watan farko a kalandar Musulunci, kuma ɗaya daga cikin muhimman watannin da Musulunci yake bai wa fifiko. A wannan wata ne al’ummar Musulmin duniya kan yi azumin nafila a ranakun 9 da 10 ga…
Read More
Yanayin kasuwa ya haifar da ƙarin farashin fetur – Kyari

Yanayin kasuwa ya haifar da ƙarin farashin fetur – Kyari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kamfanin Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ce yanayin kasuwa ne ya haifar da ƙarin farashin fetur da aka fuskanta a ranar Talata. Kyari ya bayyana haka ne yayin ganawarsu da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ranar Talata a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Ya ce sakar wa ɓangaren mai mara da aka yi, hakan zai sa a riƙa fuskantar hawa da saukar farashin man lokaci-lokaci. Shugaban na NNPCL ya ce batun ƙarin farashin fetur daga N540 zuwa N617 da aka fuskanta ba wai don ƙarancin fetur ba ne, tare da tabbatar wa 'yan…
Read More
An ƙara kuɗin fetur a Nijeriya

An ƙara kuɗin fetur a Nijeriya

A halin da ake ciki, 'yan kasuwa sun cilla farashin fetur daga N537 zuwa N617 kan lita guda a wasu gidajen mai mallakar Kamfanin Fetur na Ƙasa (NNPCL). An ga wani gidan mai mallakar NNPC s ranar Talata a Abuja yana sayar da fetur N617 kan kowace lita. Ya zuwa haɗa wannan labari babu wani bayani a hukumance daga ɓangaren NNPC ko makamancin haka dangane da ƙarin kuɗin man. Tun bayan da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin mai baki ɗaya a ranar da ya sha rantsuwar kama aiki a watan Mayu, farashin man ya cilla sama…
Read More
Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shuagaban Jam'iyyar APC na ƙasa da daga shiyyar Arewa, Abubakar Kyari, ya maye gurbin Sanata Abdullahi Adamu a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa biyo bayan murabus da Adamu ɗin ya yi. Wannan sauyin da jam'iyyar ta APC ta samu ya yi daidai da tanadin kundin dokokin jam'iyyar, wanda ya nuna cewa idan shugaban jam'iyyar na ƙasa ya yi murabus mataimakinsa ya maye gurbinsa a matsayin riƙon ƙwarya. An ga Kyari ya jagoranci mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam'iyyar wajen yin taro a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja cikin tsattsauran tsaro a ranar Litinin.…
Read More
Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Daga BASHIR ISAH Sbugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya miƙa wasiƙar yin murabus daga kujerarsa ta shugabancin jam'iyyar kamar yadda Jaridar News Point Nigeria ta rawaito. Majiyar News Point Nigeria ta bayya cewar, Sanata Adamu wanda ya zama shugaban APC a watan Maris, 2022, ya miƙa wasiƙar murabus daga muƙaminsa ga Fadar Shugaban Ƙasa gabanin dawowar Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ya halarta a ƙasar Kenya. Majiyar jaridar ta ce, Adamu ya aike da wasiƙar tasa ce ga Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, da misalin ƙarfe 4 na yammacin…
Read More
Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin sabbin hafsoshin tsaro

Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin sabbin hafsoshin tsaro

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da naɗin shugabannin hukumomin tsaro, waɗanda sabon Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa. Majalisar Dattawa Nijeriya ta tabbatar da sunayen mutanen a ranar Alhamis, 13 ga Yuli, 2023, bayan tantance su a wani zaman sirri da aka kwashe sama da awa ɗaya ana yi. Shugaban Majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya ce yayin zaman sirrin, shugabannin hafsoshin sun amsa tambayoyi kan batutuwan da suka shafi tsaro da kuma batutuwan da suka jivanci hakan. Shugaban ƙasar a cikin wata wasiƙa da aka karanta a ranar Litinin a zauren majalisar ya…
Read More
Mun gurfanar da Emefiele a kotu – DSS

Mun gurfanar da Emefiele a kotu – DSS

Daga NAISR S. GWANGWAZO a Abuja Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta bayyana cewa, ta gurfanar da dakataccen Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Mista Godwin Emefiele, a gaban kotu. Hukumar ta bayyana hakan ne a yayin da ta ke mayar da martani kan hukuncin umarnin Babbar Kotun Abuja, wacce ta umarci hukumar da ta gurfanar da shi a gaban kotu cikin mako guda ko kuma ta sake shi nan take. A yayin da Mai Shari’a Hamza Mu’azu ke yanke hukuncin kan haƙƙin bil’adama a ranar Alhamis, ya ce, cigaba da tsare mutum komai gajeren lokaci ya saɓa da haƙƙin…
Read More