21
Nov
Daga BASHIR ISAH A ranar Talata ake sa ran Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewa wanda zai gudana a jihohin Bauchi da Gombe. Aikin wanda zai gudana a yankin Kolmani shi ne irinsa na farko da Arewacin Nijerya ya taɓa gani. Kimanin shekaru biyu da suka gabata aka gano arzikin man da ke kwance a yankin. Duk da dai irin wannan aiki ba shi ne farau ba a Kudancin ƙasar, amma wannan shi zai zama karon farko Arewa bayan da matsalar tsaro ta hana aiwatar da makamacin aikin a yankin Borno. Tun a 2016…