10
Jul
An zaɓi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin sabon Shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS). Wannan ya faru ne yayin taron ƙungiyar karo na 63 wanda ya gudana a Guinea Bissau a ranar Lahadi. Wannan ne karo na farko da Tinubu ya halarci taron na ECOWAS tun bayan rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 2023. A makon jiya ne Shugaba Tinubu ya karɓi bakuncin Shugaba Embalo a birnin Legas, inda ya ce sun ci abinci tare kuma “mun tattauna kan batutuwa da dama da suka shafe mu.” A wancan lokacin, Tinubu ya ce…
