16
Apr
Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Jam'iyyar APC ta mazaɓar Dr. Abdullahi Umar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ta sanar da dakatar da Abdullahi Umar Ganduje a matsayin mamaba a jam'iyyar. Mai bai wa Jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a a mazaɓar Ganduje, Hon. Halliru Gwanzo ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Litinin. Halliru Gwanzo ya ce sun yanke shawarar dakatar da Ganduje daga jam’iyyar ne sakamakon zarge-zargen da gwamnatin Jihar Kano ta yi masa na karɓar cin hanci da rashawa. Ya ce dakatarwar ta fara ne daga daga ran 15…
