Siyasa

Masu kwaɗayin kujerar shugabancin Nijeriya su rungumi ƙaddara, Tinubu sai ya yi takwas – Ganduje

Masu kwaɗayin kujerar shugabancin Nijeriya su rungumi ƙaddara, Tinubu sai ya yi takwas – Ganduje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai ci gaba da zama shugaban Nijeriya har bayan 2027. Ganduje ya bayyana haka a lokacin da ya ke jawabi ga dandazon magoya bayan Jam’iyyar APC a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja. Ganduje ya ƙara da cewa tun ba a kai ko'ina ba jam’iyyun adawa sun fara kermar tsoron yin gaba da gaba da APC a zaɓuka masu zuwa bayan ɗan karan kayen da suka sha a zaɓen 2923. "Jam’iyyar NNPP sun fi duk jam’iyyun kiɗimewa. Sai tsalle-tsalle suke…
Read More
Ɗan majalisar Birnin Kano ya raba wa mutane 100 tallafin jari a mazaɓar Ɗan’agundi

Ɗan majalisar Birnin Kano ya raba wa mutane 100 tallafin jari a mazaɓar Ɗan’agundi

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Ɗan majalisar dokokin Jihar Kano mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Birnin Kano Hon. Ambasada Sarki Aliyu Daneji ya yi rabon tallafin jari ga al'ummar mazaɓar Ɗan'agundi. Da yake bayani game da tallafin ɗan majalisar Hon. Ambasada Sarki Aliyu Daneji ya ce tallafin na mutum 100 ne kuma da yardar Allah nan gaba za su sake dawowa su baiwa wasu duk waɗanda ba su samu a wannan karo ba su kwantar da hankalinsu har sai ya kai kowa ya dangwali romon dimukraɗiyya. Ya ce daga cikin ayyuka da ya gudanar cikin watanni 9 da zuwansu majalisar Jihar…
Read More
Kwankwaso zai ƙare rayuwarsa a fafutukar zama Shugaban Ƙasa – Lukman

Kwankwaso zai ƙare rayuwarsa a fafutukar zama Shugaban Ƙasa – Lukman

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Arewa Maso Yamma, Malam Salihu Lukman, ya ce, hanyar da Kwankwaso ya ke bi ta kaiwa ga Fadar Shugaban Ƙasa "za ta ɗauke shi shekaru masu tarin yawa wurin tattaunawa da jama'a a sassan Nijeriya, wanda zai iya wuce lokacinsa na rayuwa ma”. Lukman, wanda ya kasance baƙo a shirin siyasar gidan Talabijin na Channels a ranar Laraba, ya ce jam’iyya mai mulki za ta iya hanzarta aiwatar da muradin Kwankwaso ta hanyar buɗe masa ƙofar jam’iyyar domin ya dawo ya sake gina gada da aka ƙona a…
Read More
Bayan shekara 26, tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha ya fice daga PDP

Bayan shekara 26, tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha ya fice daga PDP

Daga BASHIR ISAH Bayan shafe shekara 26 a matsayin mabiyin jam'iyyar PDP, tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, ya sauya sheƙa daga jam'iyyar zuwa wata. Ihedioha ya ce ya fice daga jam'iyyar ta PDP ne bisa ra'ayinsa. A cewarsa, abin takaici ne ganin yadda PDP ta ɗare kan turbar da ta saɓa wa ra'ayinsa. Ya ce, "Duk da ƙoƙarin da na yi na bai wa jam'iyyar shawarwari, jam'iyyar ta kasa samar da sauye-sauyen cigaba a cikin gida, tabbata ra da kiyaye dokokinta, ko kuma zama 'yar hamayya mai ƙarfi ga jam'iyyar APC mai mulki. “Bisa wannan dalili ne na rage…
Read More
Masu burin kassara PDP ke adawa da shugabancin Umar Damagun – Biniya Gabari

Masu burin kassara PDP ke adawa da shugabancin Umar Damagun – Biniya Gabari

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An zargi wasu ‘yan majalisar wakilai 60 na PDP da wasu ƙungiyoyin da ke nuna adawa da shugabancin Ambasador Umar Iliyasu Damagun a matsayin shugaban riƙo na jam’iyyar na ƙasa, da kasancewa karnukan farauta ne da ake amfani da su wajen yin zagon ƙasa ga ci gaban jam’iyyar. Shugaban haɗakar matasa na jam’iyyar na ƙasa PDP Youths Collation Movement Hon. Biniya Yahuza Gabari ya bayyana haka. Ya ƙara da cewa ‘ya’yan  jam'iyyar su ke ƙalubalantar shugaban riƙo na jam'iyyar PDP na da   ɓoyayyen manufa na ruguza jam’iyyar ne, ganin yanda yanzu take samun ƙarin goyon…
Read More
Dalilin da ya sa na daina saka baki a siyasar Nijeriya – Rotimi Amaechi

Dalilin da ya sa na daina saka baki a siyasar Nijeriya – Rotimi Amaechi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Ministan Sufuri a Nijeriya Rotimi Amaechi ya ce an daina jin ɗuriyarsa ne a fagen siyasar Nijeriya saboda "babu wani sabon abu" da zai faɗa. Tsohon gwamnan na jihar Ribas ya riƙe muƙamin minista a gwamnatin tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari daga 2015 zuwa 2022, bayan ya mulki jihar tasa a Kudancin Nijeriya tsawon shekara takwas. "Babu wani sabon abu kwatakwata," inji ɗan siyasar wanda ya nemi takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar APC mai mulki cikin hira ta musamman da BBC. "Abubuwan da ake so na yi magana a kan su suna nan…
Read More
Yadda tuhume-tuhume suka kaure tsakanin Abba da Ganduje

Yadda tuhume-tuhume suka kaure tsakanin Abba da Ganduje

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Tataɓurza, musayar yawu da kuma tayar da ƙura irin na siyasa sun kunno kai a Jihar Kano tsakanin  zaɓaɓɓen gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-gida) da kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Shugaban Jam'iyyar APC ta Ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Gumurzun ya fara ne daidai lokacin da Jam’iyyar APC reshen mazavlɓar Ganduje da ke Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano ta dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.  Mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a a mazaɓar Ganduje, Haladu Gwanjo, ne ya sanar da dakatar da…
Read More
Atiku da Wike sun halarci babban taron jam’iyyar PDP a Abuja

Atiku da Wike sun halarci babban taron jam’iyyar PDP a Abuja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Laraba ne ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Alhaji Atiku Abubakar da ministan babban birnin tarayya, Nyesome Wike, suka halarci taron jam’iyyar PDP na ƙasa a Abuja gabanin kwamitin zartarwa na jam’iyyar na ƙasa. Wannan dai shi ne karon farko da tsohon gwamnan jihar Ribas zai halarci taron jam'iyyar PDP tun bayan zaɓen shugaban ƙasa a bara. Wike dai ya samu saɓani da shugabannin jam’iyyar PDP kuma bai goyi bayan zaɓen Abubakar da jam’iyyar ta yi ba a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaven bara. Baya ga…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Babbar Kotun Jihar Kano mai Lamba 4 dake zaman ta a kan titin Mila, ta tabbatar da dakatarwar da wasu shugabannin Jam'iyyar APC a Mazaɓar Ganduje suka yi wa Shugaban Jam'iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje daga jam'iyyar. Alƙalin Kotun, Justice Usman Malam Na'abba ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata takardar da masu ƙara suka nema, ba tare da sanar wa ɓangaren waɗanda suke ƙara ba wato (Motion Ex parte). Haladu Gwanjo da Laminu Sani ne suka shigar da ƙarar, inda suka yi ƙarar ɓangarori huɗu waɗanda suka haɗar da Jam'iyyar APC, Kwamitin…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe Sakataren PDP a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe Sakataren PDP a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan bindiga da ake zargin ɓarayin daji ne a Jihar Zamfara, sun kashe Sakataren Jam'iyyar PDP na Ƙaramar Hukumar Tsafe a jihar, Musa Ille. Majiyarmu ta ce an kashe marigayin ne a ƙofar gidansa bayan da da 'yan bindigar suka yi wa gidan ƙawanya a ranar Litinin da daddare. Shugaban PDP na yankin, Garba Garewa, shi ne ya tabbatar da faruwar hakan ga manema labarai a ranar Talata. Ya ce, “Muna zargin makisan 'yan fashin daji ne, jiya (Litinin) suka shiga gidansa suka halbe shi." Wani mazaunin yankin, Abubakar Tsafe, ya shaida wa jaridar News Point…
Read More