Wasanni

’Yar damben Nijeriya ta faɗi gwajin ƙwayar ƙara kuzari a Olympics

’Yar damben Nijeriya ta faɗi gwajin ƙwayar ƙara kuzari a Olympics

An dakatar da ’yar wasan damben Nijeriya, Cynthia Ogunsemilor daga gasar Olympics bayan da ta gaza tsallake gwajin shan ƙwayar ƙara kuzari. Gwajin da aka yi wa Ogunsemilor, wadda ta samu lambar yabo ta zinare a wasan 'Africa Games' a birnin Accra a farkon shekarar nan da kuma tagulla a gasar commonwealth a Birmingham, ya nuna tana shan furosemide, ƙwayar da aka haramta sha. Hukumar da ke bincike kan amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari tsakanin ’yan wasan motsa jiki ce ta yi gwajin a ranar 25 ga watan Yuli a madadin kwamitin shirya gasar Olympics. ’Yar wasan mai shekara 22…
Read More
Hukumar NFF na neman wanda zai zama kocin Flying Eagles

Hukumar NFF na neman wanda zai zama kocin Flying Eagles

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ta bazama neman wanda ya cancanta domin zama kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta ’yan ƙasa da shekaru 20, wanda aka fi sani da Flying Eagle. Sanarwar da NFF ta fitar ta ce, “Ga duk wanda yake neman zama kocin tagawar, to ya ziyarci shafin intanet na Hukumar - (https://thenff.com/job/ɓacancy-for-the-position-of-u-20-male-national-team-head-head) -coach/), ya saka duk bayanansa, sannan ya zama yana da aƙalla lasisin CAF B, dole ne kuma ya kasance a aikin horar da ƙwallon ƙafa na aƙalla shekaru biyar, ya kasance mai ƙwararre a wasannin cikin gida na Nijeriya, mai kyawawan halaye na jagoranci da…
Read More
NFF ta bada sanarwar neman sabon kocin Flying Eagles

NFF ta bada sanarwar neman sabon kocin Flying Eagles

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya ta fitar da sanarwar neman sabon kocin Flying Eagles. Wannan sanarwa ta fito ne a shafin ta na yanar gizo, inda ta ke neman wanda zai jagorancin ƙungiyar Flying Eagles wanda sune yan ƙasa da shekaru 20. Sanarwar ta bayyana cewa duk mai sha'awar neman aiki, dole ya zama yayi koci aƙalla na shekara biyar sannan ya saba da gasar cikin gida ta Nijeriya da kuma lasisin CAF B na koci. Duk mai neman aiki zai iya zama ɗan Nijeriya cikin gida ko a waje. Za a rufe shafin yanar gizon neman aikin, 14 ga…
Read More
Gwamnan Kano ya amince da naɗin sabbin shugabannin Kano Pillars

Gwamnan Kano ya amince da naɗin sabbin shugabannin Kano Pillars

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin sabbin shugabannin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars. Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanar ranar Lahadi. Ya bayyana za su aiki na tsawon shekara guda sannan a duna yiyuwar ƙara musu wa'adi ganin ƙoƙarin ƙungiyar. Sabbin shugabannin sun haɗa da; Ali Muhammad Umar (Nayara Mai Samba) – Shugaba – Salisu Kosawa – Yusuf Danladi (Andy Cole) – Nasiru Bello – Muhammad Ibrahim (Hassan West) – Muhammad Usman – Muhammad Danjuma Gwarzo – Mustapha Usman Darma – Umar Dankura – Ahmad Musbahu – Rabiu Abdullahi – Abubakar…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Bologna na tattaunawa da ɗan bayan Jamus Mats Hummels, mai shekara 35, wanda ba shi da ƙungiya bayan da ya bar Borussia Dortmund, yayin da ƙungiyar ta Italiya ke neman wanda zai maye gurbin Riccardo Calafiori mai shekara 22, wanda ke shirin tafiya Arsenal. Getafe za ta samu sama da fam miliyan 5 ne kawai daga cinikin sayar da Mason Greenwood fam miliyan 26.7 daga Manchester United zuwa Marseille, saboda yaerjejeniyar da suka yi lokacin da suka karɓi aron ɗan wasan na Ingila mai shekara 22 daga Old Trafford a bara. Ɗan gaban Scotland Oli McBurnie, mai shekara 28, na…
Read More
Sifaniya ta taki matsayi na uku a sabon jadawalin FIFA

Sifaniya ta taki matsayi na uku a sabon jadawalin FIFA

Wannan jerin jadawalin yana zuwa ne bayan shafe wata guda ana buga wasanni, inda Argentina ta lashe kofin Copa America bayan da ta doke Colombia, yayin da Sifaniya ta lashe European Championship bayan ta doke Ingila. Ingila ta koma ta huɗu, bayan da tawagar Brazil da ta ƙasa taɓuka abun kirki a gasar kofin Copa America da aka yi a Amurka, ta koma ta biyar. Ɓenezuela, wacce ta kai wasan daf kisa da ƙarshe a gasar Copa America ta zama ƙasar da ta fi samun ci gaba a jadawalin, bayan da ta tsallake matsayi 17 ta zama 37, yayin da…
Read More
Tawagar Super Falcons ta shirya tunkarar gasar Olympics – Waldrum

Tawagar Super Falcons ta shirya tunkarar gasar Olympics – Waldrum

Mai horas da Tawagar Ƙwallon Ƙafa ta Mata ta Nijeriya Randy Waldrum, ya ce tawagar ta  shirya don tunkarar gasar Olympics da birnin Paris zai kar baƙunci, duk kuwa ta makarar zuwa sansani da wasu ’yan wasa suka yi. A wata zantawa da aka yi da shi, Waldrum ya ce duk da rashin isowar wasu daga cikin ’yan wasan tawagar akan lokaci, amma sun yi ƙoƙarin sajewa da sauran da suka iso da wuri. Wannan ne dai karo na farko a cikin shekaru 16 da tawagar ta samu gurbin buga gasar Olympics, inda ta kasance daya daga cikin tawagogin ƙasashen…
Read More
Jerin ’yan wasan da a ke sa ran ɗayan su zai lashe kyautar Ballon d’Or ta bana 

Jerin ’yan wasan da a ke sa ran ɗayan su zai lashe kyautar Ballon d’Or ta bana 

A ranar 4 ga Satumba za a sanar da jerin waɗanda za su yi takarar zama gwarzon Ɗan Wasan Ƙwallon Ƙafa na duniya, inda za a yi la'akari da kakar wasa ta 2023-24 tare da kuma manyan gasa da aka gudanar a bazara. Yayin da Ɓinicius Jr da Jude Bellingham na Real Madrid suka kasa lashe gasar kofin nahiya da suka buga da Brazil da Ingila, hakan na nufin kambun ya zama na mai rabo ka ɗauka. Ga jerin 'yan wasa shida da ake sa ran ɗayan su zai iya yin nasara a bikin da za a yi a ranar…
Read More
Argentina ta lashe gasar Copa America karo na 16

Argentina ta lashe gasar Copa America karo na 16

Argentina ta doke Kolombiya inda ta lashe gasar kofin Copa America karo na 16, sai dai wasan ya samu tsaiko bayan anjinkirta na tsawon mintuna 80 saboda hargitsi a wajen filin wasa na Hard Rock. Lautaro Martinez ne ya samu nasarar zurawa Argentina ƙwallo ɗayan, da ta ba ta wannan nasarar a mintina na 112, mintina bakwai kafin bugun daga kai sai mai tsaron raga. Kyaftin Lionel Messi ya sha kuka lokacin da aka maye gurbinsa a mintina 66 da fafatawa, bayan raunin da ya samu a idon sawunsa. Masu shirya gasar sun ce magoya bayan da ba su da…
Read More
Yadda aka ƙarƙare gasar Euro 2024

Yadda aka ƙarƙare gasar Euro 2024

Sifaniya ta zama ta farko da ta lashe gasar kofin nahiyar Turai karo huɗu a tarihi, bayan da ta doke Ingila 2-1 ranar Lahadi. A minti na uku da suka koma zagaye na biyu ne Sifaniya ta ci ƙwallo ta hannun Nico Williams, bayan da Lamine Yamal ya zura masa ƙwallon. To sai dai Ingila ta farke ta hannun Cole Palmer, bayan da Jude Bellingham ya ajiye masa ƙwallon a ƙasa, saura minti 27 a tashi daga fafatawar. Saura minti biyar a tashi daga karawar Sifaniya ta ƙara na biyu ta hannun Mikel Oyarzabal. Da wannan sakamakon Sifaniya ta lashe…
Read More