24
Aug
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya, NFF, ta kusa kawo ƙarshen taƙaddamar da ake yi kan zaɓen wanda zai cigaba da jan ragamar horar da ’yan wasan Super Eagles na Nijeriya, duk da cewa har yanzu akwai tsaikon da ake fuskanta kan cire caya daga cikin mutane biyu da suka rage. Tawagar Super Eagles ba ta da koci tun bayan da Finidi George ya ajiye aikinsa bayan wasa biyu kacal a cikin kwatiraginsa ta shekara biyu. Finidi yana cikin ’yan wasan Nijeriya da suka lashe Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (Afcon) ta shekarar 1994, sannan ya taɓa riƙe matsayin na riƙon…
