12
Apr
Daga WAKILINMU Rahotanni sun tabbatar cewa fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafar nan kuma kyaftin a Super Eagles, wato Ahmed Musa, na shirin sake komawa ƙungiyar Kano Pillars don yin aiki na taƙaitaccen lokaci. Musa, ɗan shekara 28, ya kasance ba ya buga ma wata kulob wasa tun daga Otoban 2020, bayan kammala harƙallarsa da ƙungiyar Al Nassr ta ƙasar Saudiyya, bayan kuma ya kasa samu ƙulla wata harka a Turai. Bayanai sun nuna ana sa ran tsohon ɗan wasan Leicester City ɗin zai yi aiki na ɗan lokaci tare da Kano Pillars. Kanawa na matuƙar martaba ɗan wasan tun bayan…