Wasanni

An cire Ronaldo daga cikin ‘yan wasan Portugal da za su fafata da Nijeriya

An cire Ronaldo daga cikin ‘yan wasan Portugal da za su fafata da Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Tawagar Ƙwallon Ƙafar Portugal Fernando Santos ya ce, Cristiano Ronaldo baya cikin ’yan wasan da za su fafata da Super Eagles ta Nijeriya a wasan sada zumunta a yau alhamis ba sobado yana fama da ciwon ciki. Ɗan wasan mai shekaru 37, wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or sau biyar, bai yi atisaye a ranar Laraba ba, saboda rashin lafiyar da ta faro cikin yanayi na cece-kuce da ake yi kan hirarsa da Piers Morgans inda ya caccaki Manchester United. Tuni aka cire hotunan Ronaldo daga bangon filin wasan Manchester United wato Old Trafford a…
Read More
Ba zan bar Liverpool ba koda an sayar da ƙungiyar, inji Klopp

Ba zan bar Liverpool ba koda an sayar da ƙungiyar, inji Klopp

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin ƙungiyar Liverpool, Jurgen Klopp ya ce, yana nan kan aikin ƙungiyar ko me zai faru ga waɗanda za su mallaketa a gaba. Tawagar Fenway Sports Group (FSG) ta ce, tana neman sabbin masu zuba jari, sai dai wasu rahotanni na cewa suna son sayar da ƙungiyar ne baki ɗaya. Matakin dai ya janyo fargaba da cece-kuce tsakanin magoya bayan Liverpool inda ake tsoron rikici a Anfield, kuma hakan ya janzo tambaya kan makomar kocinta Klopp. A ranar Laraba, Liverpool ta doke Derby County a bugun fenareti a wasan Carabao. Da ya ke bayani karon farko…
Read More
Drogba ya musanta karɓar addinin Musulunci

Drogba ya musanta karɓar addinin Musulunci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafar Ivory Coast, Didier Drogba ya musanta labarin da ke cewa ya karɓi addinin Musulunci. Wannan na zuwa ne bayan da wani malami ya wallafa hotonsa tare da tsohon ɗan ƙwallon suna addu’a a shafinsa na Tuwita. Kotu Ta Daure Barawon Awaki A Gidan KasoMalamin ya wallafa hoton, tare da cewa tsohon ɗan ƙwallon ya musulunta. To sai dai a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Tuwita, Drogba ya ce ba musulunta ya yi ba, addu’a kawai ya ke yi wa musulman ƙauyensu bayan da ya ziyarci ƙauyen nasu. Ya…
Read More
Flamingos sun sauka a Abuja bayan lashe tagulla a gasar kofin duniya ta mata

Flamingos sun sauka a Abuja bayan lashe tagulla a gasar kofin duniya ta mata

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ’Yan wasan Flamingos sun sauka a Abuja, babban birnin Nijeriya bayan da suka lashe kyautar tagulla a gasar kofin duniya ta mata ’yan ƙasa da shekara 17 da aka yi a Indiya. Nijeriya ta doke Jamus a bugun fenariti bayan da aka tashi 3-3 a wasan neman gurbi na uku a gasar. Tawagar ’yan wasan ta sauka a filin tashin jirage na Nnamdi Azikwe a ranar Talata inda jami’an hukumar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta NFF suka tarbe su. Jim kaɗan bayan saukarsu, ministan wasanni da matasa, Sunday Dare, ya gana da ’yan wasan inda ya ba…
Read More
Za a ɗaure ɗan wasan Jamus, Jerome Boateng da laifin dukan budurwarsa

Za a ɗaure ɗan wasan Jamus, Jerome Boateng da laifin dukan budurwarsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kotu a Jamus ta tabbatar da laifin cin zarafi kan fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafar ƙasar Jerome Boateng, wanda ake tuhuma da laifin dukan tsohuwar budurwarsa a shekarar 2018. A shekarar da ta gabata ne kotu ta samu Boateng da laifin cin zarafin tsohuwar abokiyar zamansa, mahaifiyar ’ya’yansa tagwaye mata, a lokacin hutun Caribbean shekaru huɗu da suka wuce, makwanni bayan kammala gasar cin kofin duniya a Rasha. Sai dai kotun da ke gundumar Munich ta rage yawan tarar da a baya aka buƙaci Jerome Boateng ya biya daga Yuro miliyan 1.8 zuwa Yuro miliyan 1.2.…
Read More
Pique zai yi ritaya daga buga wasan ƙwallon ƙafa gobe

Pique zai yi ritaya daga buga wasan ƙwallon ƙafa gobe

Daga NASIR S. GWANGWAZO Ɗan wasan baya na Ƙungiyar Barcelona, Gerard Pique, ya bayyana shirinsa na yin ritaya daga wasan ƙwallon ƙafa bakiɗaya a gobe Asabar bayan kammala wasan ƙungiyar tasa da Almeria, wanda zai zamo shine wasansa na ƙarshe a tarihi. Pique, mai shekaru 35, ya bayyana hakan ne a kafafensa na sadarwar zamani cikin wani bidiyo a jiya Alhamis. Ɗan wasan tsakiyar bayan dai sau uku kacal Barcelona ta saka shi a jerin ’yan wasa 11 na farko a kakar wasa ta bana, inda matasan ’yan wasa irinsu Ronald Araujo, Jules Kounde, Andreas Christensen da Eric Garcia suke…
Read More
Tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Super Eagles da Kano Pillars, Bello Musa ya rasu

Tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Super Eagles da Kano Pillars, Bello Musa ya rasu

Daga BASHIR ISAH Rahotanni sun ce Bello Musa Ƙofarmata ya rasu ne ranar Talata a mahaifarsa, Kano yana da shekara 34. Tuni aka yi jana'izar marigayin a Kano daidai da karantarwar Musulunci. Bayanai sun nuna Musa ya soma harkar ƙwallon ƙafa ne a 2007 a kulob ɗin Buffalo da ke Kano, daga bisani ya samu shiga ƙungiyar Kano Pillars. A 2010 ya sauya sheƙa zuwa ƙungiyar Heartland a Owerri sannan ya sake dawowa Kano Pillars a 2012, kana daga bisani ya tafi ƙungiyar Elkanemi Warriors a Maiduguri. Bayan wasu lokuta marigayin ya samu kwantiragi da kulob ɗin IK Start a…
Read More
An caccaki Ƙatar kan cin zarafin baƙi gabanin gasar Kofin Duniya

An caccaki Ƙatar kan cin zarafin baƙi gabanin gasar Kofin Duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ƙasashe da babbar tawagar ƙwallon ƙafar Australiya sun caccaki jerin cin zarafin bil adama a Ƙatar, gabanin Gasar Kofin duniya da ke tafe a watan Nuwamban wannan shekarar, lamarin da ya sa Australiya kasance tawaga ta farko da ke cikin wannan gasa da ta caccaki ƙasar da ke karɓar baƙuncin gasar. Gasar Kofin Duniya da za a fara a ranar 20 ga watan Nuwamba ta fuskanci cece-kuce tun daga lokacin da aka bai wa Ƙatar damar karɓar baƙuncin shekaru 12 da suka wuce. Hukumar ƙwallon ƙafar Australia ta ce ta san cewa an yi sauye-sauye…
Read More
FA ta ci tarar kocin Liverpool Yuro 30,000

FA ta ci tarar kocin Liverpool Yuro 30,000

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar FA ta ci tarar kocin Liverpool, Jurgen Klopp Yuro 30,00 bayan jan katin a wasan da ƙungiyarsa ta yi nasara a kan Manchester City a ranar 16 ga watan Oktoba. An kori Klopp daga filin wasa bayan rashin ɗa'ar da ya yi wa mataimakin alƙalin wasa, lokacin da aka ƙi bai wa Mohamed Salah damar dukan da aka yi masa. Kocin ya nemi afuwa kan halayyar da ya nuna bayan an tashi daga wasa. "Wani abu ne ya ɗauki hankali ne, ba alfahari na ke ba. Na cancanci jan kati," a cewarsa. An tuhumi Klopp…
Read More
FIFA U17: Flamingos ta kai mataki na kusa da ƙarshe

FIFA U17: Flamingos ta kai mataki na kusa da ƙarshe

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Mata ta Nijeriya (Flamingos) ta samu nasarar tsallakewa zuwa mataki na kusa da ƙarshe na gasar Kofin Duniya na FIFA na mata 'yan ƙasa da shekara 17 wanda ke gudana a Indiya. Flamingos ta samu wannan nasara ne bayan da ta lallasa takawararta ta Amurka da ci 4-3 a bugun fenariti. An buga wannan wasa ne a ranar Juma'a, 21 ga Oktoba, 2022.
Read More