Month: February 2021

Hajjin 2021: Babu kujerar Hajji da aka bai wa Nijeriya – inji NAHCON

Hajjin 2021: Babu kujerar Hajji da aka bai wa Nijeriya – inji NAHCON

Daga BASHIR ISAH Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta kore batun da aka yi ta yayatawa wai ta samu kujerun Hajji daga Gwamnatin Saudiyya na Hajjin bana. Sanarwar da hukumar NAHCON ta fitar a Juma'ar da ta gabata wadda ta samu sa hannun shugabar sashen hulɗa da jama'a ta hukumar, Fatima Sanda, ta nuna hankalin hukumar ya kai ga wani saƙon talla da aka yi ta yaɗawa a soshiyal midiya kan cewa Nijeriya ta samu gurbin mahajjata 50,000 na Hajjin 2021/1442 AH a hukumance. Tallar ta buƙaci maniyyata Hajji suna iya soma ajiyar wani kaso na kuɗi don sayen kujerar…
Read More
An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

Daga FATUHU MUSTAPHA Bayanai daga Jihar Neja sun nuna an sako ɗalibai da malamai na Sakandaren Kimiyya Kagara da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su 'yan kwanakin da suka gabata. Wata majiya mai tushe ta tabbatar wa jaridar PRNigeria batun sakin ɗaliban a safiyar wannan Asabar. Idan dai za a iya tunawa, Manhaja ta ruwaito batun sace ɗaliban su 27 da ma'aikata 3 da iyalansu su 12, a ranar 17 ga Fabrairun 202.
Read More
Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Daga IBRAHIM SHEME A ranar Litinin da ta gabata, sabon shugaban Hukumar Yaƙi da Safara da Shan Muggan Ƙwayoyi (NDLEA), Janar Mohammed Buba Marwa (ritaya), ya yi wata magana wadda ya kamata ta farkar da duk ɗan Nijeriya game da matsalar da fataucin muggan ƙwayoyi ke janyo wa ƙasar nan. Cewa ya yi kashi 90 cikin ɗari na muggan laifukan da ake aikatawa a Nijeriya, sakamakon ɗirkar muggan ƙwayoyi da wasun mu ke yi ne. A cewar sa, laifuka irin su hare-haren ‘yan bindiga, ta’adda, satar mutane, fyaɗe da sauran su duk ‘yan ƙwaya ne ke aikata su. Marwa, wanda…
Read More
Minista Dare ya ƙaddamar da gasar ‘Principal Cup’

Minista Dare ya ƙaddamar da gasar ‘Principal Cup’

Daga BASHIR ISAH An ƙaddamar da gasar ƙwallon ƙafa na 'Principal Cup'. Ministan Matasa da Wasannin Motsa Jiki, Mr Sunday Dare ne ya ƙaddamar da gasar a birnin Legas a wannan Juma'a. Bayan ƙaddamar da gasar, Igbobi da kuma Government College Kaduna, su ne suka fara fafatawa a filin wasannin motsa mitsa jiki na Agege, Legas. A cewar Minista Dare wanda shi ne silar farfaɗo da gasar 'Principal Cup', " Cikar buri ne kuma abin farin ciki ganin wannan gasa ta kankama a yau. "Muna alfahari da wasan da waɗannan matasa suka yi a yau. Ina fata wannan zai zama…
Read More
Yadda na samu kaina a harkar fim, Saratu Giɗaɗo (Daso)

Yadda na samu kaina a harkar fim, Saratu Giɗaɗo (Daso)

Fitacciyar jaruma a masana’antar shirya finafinai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi sani da sunan Daso, jaruma ce da ta daɗe ana damawa da ita a cikin masana’antar, wadda a yanzu idan ana maganar dattawan cikin harkar fim to Saratu za ta iya shigowa cikin su.Tsawon shekarun da ta shafe a matsayin ba tare da an daina yayin ta ba ya kai ta ga zama kaɗan daga cikin jaruman da su ka kafa tarihi a cikin masana’antar domin wasu ɗan lokaci kaɗan su ke ci sai a daina ganin su, ko dai a ce sun bar harkar, ko kuma…
Read More
Ba a koyon rubutu, ba a sayen sa da kuɗi – Jamila Rijiyar Lemu

Ba a koyon rubutu, ba a sayen sa da kuɗi – Jamila Rijiyar Lemu

Jamila Abdullahi Rijiyar Lemu ƙwararriyar marubuciya ce da ta daɗe tana jan zaren ta a duniyar rubuta littattafan Hausa.  Kuma ta yi zarrar zuwa ta biyu a gasar da sashen Hausa na BBC ke shirya wa mata zalla a duk shekara, wato ‘Hikayata,’ a shekarar 2019. A wannan tattaunawar da wakiliyar Manhaja, za ku ji yadda marubuciyar ta sha gwagwarmaya da faɗi-tashi a harkar rubutu. Daga AISHA ASS Mu fara da jin tarihin ki a taƙaice.Bismillahir Rahmanir Rahim! Suna na Jamila Abdullahi Rijiyar Lemu. An haife ni a shekara ta 1980. Na yi karatu tun daga firamare zuwa Jami’ar Bayero…
Read More
Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Tallafin naira biliyan 600 ga manoma

Labarin da aka bayar cewa Gwamnatin Tarayya na shirin bada tallafin sama da naira biliyan 600 don agaza wa manoma abin farin ciki ne. Ba shakka, abin da ya dace ne idan har ana so a faɗaɗa hanyoyin inganta tattalin arzikin ƙasar nan, wanda ya shafe sama da shekara hamsin ya na dogaro da man fetur wajen samun kuɗaɗen shiga. Ministan Aikin Gona Da Raya Yankunan Karkara, Alhaji Sabo Nanono, shi ne ya bayyana labarin a cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na ma’aikatar sa, Mista Theodore Ogaziechi, ya rattaba wa hannu kwanan nan a Abuja. A sanarwar, an…
Read More

Zawiyyoyi da gudunmawar su wajen ilmantarwa da inganta rayuwar al’umma

Daga Tahir Lawan Muaz Attijaneey Gabatarwa: Da sunan Allah, mai rahama mai jinƙai, tsaira da amincin Allah su tabbata ga Shugaban Talikai Sayyadina Rasulillahi ɗan Abdullahi da Aminatu, tare da Ahlin gidansa tsarkaka da Sahabbansa baki ɗaya. Bayan haka, wannan maudu’i da aka ba ni na yi bayani a kansa ƙarƙashin wannan mu’asasah ta AL-SUFF FOUNDATION yana da matukar faɗi, hasali ma idan muka ɗauke shi gaɓa gaɓa za muga ya ƙunshi ɓangarori biyu manya wato bayani kan zawiya sai kuma gudunmawarsu wajen ilmantarwa da inganta rayuwa. Har ila yau, idan muka koma za mu ga cewa shin ana so…
Read More