Editor

9513 Posts
Yadda za ki kula da fatarki a lokacin sanyi (4)

Yadda za ki kula da fatarki a lokacin sanyi (4)

Daga AISHA ASAS A ci gaba da bayyani kan yadda za a iya ba wa fata kulawa a lokacin sanyi, a yau darasin namu zai tabo bangaren gashi. Sai dai kafin nan zan so mu yi waiwaye don tunatar da mai karatu abinda darasin namu ya kunsa a baya. Mun soma da bayanin yadda fata ke shiga mawuyacin hali a lokutan sanyi, wanda muka ce da taimakon sanin yadda ake iya kula da ita, za a samu sauqi daga irin lalacewar da ta ke yi a lokacin sanyi. Sannan mun kawo hanyoyin da za a iya kula da fatar daga…
Read More
Dandalin shawara: Mijina ba ya iya gamsar da ni kuma na rasa ta yadda zan sanar da shi

Dandalin shawara: Mijina ba ya iya gamsar da ni kuma na rasa ta yadda zan sanar da shi

Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Assalamu alaikum. Malama barka da rana. An wuni lafiya. Ya iyali. Allah shi taimaka maki, amin. Ni dai tambaya ta dai ina neman yadda zan sanar da mijina ba ya wadatar da ni a shimfida. Wato shi dai mutumin kirki ne sosai, yana iya kar kokari ga iyalinshi, tun ma ba akan abinci ba daidai gwargwado muna ci mu koshi. Yana wasa da dariya da dai sauran abubuwa. To amma matsalar ba shi da wani karfi. Tun da aka kawo ni gidansa a matsayin budurwa babu jimawa na daina koshi da rayya sunnah da muke yi,…
Read More
Matsalar tsaro: Majalisar Dattawa za ta sammaci Ministan Abuja

Matsalar tsaro: Majalisar Dattawa za ta sammaci Ministan Abuja

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta ce ta kimtsa domin gayyato Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya zo ya yi bayani game da tabarbarewar tsaro a Birnin Tarayya. Sanata mai wakiltar Birnin Tarayya a Majalisar, Ireti Kingibe ce ta bayyana haka yayin wata tattaunawa da tashar Channels TV ta yi da ita a ranar Lahadi. Ta ce idan majalisar ta dawo bakin aiki, za a gayyato Wike a matsayinsa na Ministan Abuja don ya zo ya yi bayanin matakan da yake dauka domin dakile matsalar taro a birnin na tarayya. A cewar Sanatar, “Ina da yakinin za a gayyace shi. Amma…
Read More
Kotu ta ayyana Kasafin 2024 na Jihar Ribas haramtacce

Kotu ta ayyana Kasafin 2024 na Jihar Ribas haramtacce

Babbar Kotun Tarayya a Abuja, ta  bayyana kasafin 2024 na Jihar Ribas a matsayin mara inganci kuma haramtacce. Kotun ta haramta kasafin ne a zaman shari’ar da ta yi a ranar Litinin karkashun jagorancin Mai Shari’a James Omotosho. A cewar Kotun, kasafin ya zama haramtacce ne saboda rashin ingancinsa da kuma saba tsari da aka yi kafin gabatar da shi a gaban Majalisar Dokokin Jihar. Kotun, wadda ta ayyana Martin Amaewhule a matsayin halastaccen Shugaban Majalisar, ta kama Gwamna Fubara da laifin yi wa Majalisar Dokoki na jihar katsalandan cikin harkokinta. Alkali Omotosho ya ce Gwamnan jihar ba shi da…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta sahale wa kamfanoni bakwai da su rarraba man Ɗangote

Gwamnatin Tarayya ta sahale wa kamfanoni bakwai da su rarraba man Ɗangote

Daga AMINA YUSUF ALI A halin yanzu dai manyan kamfanonin dillancin mai guda bakwai da muke da su a Nijeriya sun yi rajista tare da kamfanin tace man Dangote domin rarraba tataccen mai ta hanyar sara da sarar da shi. Wato dai man fetur din da matatar Dangoten wacce aka gina ta a kan Naira biliyan 20 ta samar. A ranar Lahadin da ta gabata ne dai su wadannan kamfannin dillancin a qarqashin shugabancin Kungiyar Manyan dillalan Man feturta Nijeriya (MOMAN) ita ce ta tabbatar da cewa,  bayan yin rajistar tasu, za su iya cigaba da rarraba man fetur din…
Read More
An damƙe ɗaya daga cikin masu garkuwa da suka addabi Abuja

An damƙe ɗaya daga cikin masu garkuwa da suka addabi Abuja

Rundunar ‘Yan Sandan Birnin Tarayya (FCT) ta tabbatar da cafke wani gawurtaccen mai garkuwa da mutane, Chinaza Phillip, wanda ake zargin yana daya daga cikin batagarin da suka addabi yankin Abuja da sace-sacen mutane. Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ta ce sun kama wanda ake zargin ne a  ranar Alhamis a Jihar Kaduna. Ta kara da cewa, a ranar Juma’ar da ta gabata aka mika wa rundunar Chinaza Phillip wanda a halin yanzu ake ci gaba da tsare shi. Cikin sanarwar da ta fitar, rundunar ta ce, “Rundunar ‘Yan Sandan FCT na sanar da cewa, jami’an ‘yansanda a jihar Kaduna…
Read More
‘Yan gida ɗaya da aka yi garkuwa da su a Abuja sun shaƙi iskar ‘yanci

‘Yan gida ɗaya da aka yi garkuwa da su a Abuja sun shaƙi iskar ‘yanci

‘Yan matan nan ‘yan gida daya da aka yi garkuwa da su tare da mahaifinsu a yankin Abuja, sun shaki iskar ‘yanci. A farkon watan Janairun da ake ciki ne ‘yan fashin dajin suka yi garkuwa da wadanda lamarin ya shafa, inda sakamakon jinkirin da aka yi wajen biyan kudin fansar da ‘yan bindigar suka nema, daya daga cikin yaran mai suna Nabeeha ta rasa ranta. A karshen mako ne aka ga isowar ‘yan matan gidansu da ke Abuja bayan da aka ceto su daga hannun ‘yan bindigar. Bayanai sun ce yaran sun koma gida ne bisa rakiyar jami’an tsaro…
Read More
Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan 1

Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan 1

Manufar Gwamnatin Tarayya na samar da Dala Tiriliyan 1 na tattalin arzikin kasa ba zai yiwu ba idan har aka cigaba da samun tabarbarewar matsalar rashin tsaro a kasar. Mafita ita ce jami’an tsaro su gaggauta daukar mataki tare da tabbatar da cewa an fatattaki ’yan bindiga da sauran miyagun da ke ta’addanci a kasar. Shugaba Bola Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga hafsoshin tsaro da shugabannin hukumomin leken asiri a wani taron tsaro da shugaban kasa ya gudanar kwanan nan a fadar shugaban kasa da ke Abuja. A cewar shugaban, yayin da ake samun…
Read More
Mu mayar da hankali ga yin gwaji kafin aure

Mu mayar da hankali ga yin gwaji kafin aure

Tare da ABBA ABUNAKAR YAKUBU Zainab wata matashiya ce da ke koyon aikin jinya, kuma take daf da daidaita zancen aure tsakaninta da wanda take so ta aura. Sanin muhimmancin yin gwajin kwayoyin halittar jini ga aurenta, ya sa ta garzaya domin duba nau'in kwayar halittar jininta a wani asibiti da ke cikin garin Katsina. Sai dai ga mamakinta sakamakon da ya fito ya tsoratata ganin cewa tana dauke ne da nau'in genotype mai AS, savanin abin da take sa rai ta gani na AA, wanda a cewarta akasari 'yan gidansu ke da shi. Babu shakka wannan sakamako ya girgiza…
Read More
Ba zan taɓa cin amanar Kwankwaso ba – Abba Gida-gida

Ba zan taɓa cin amanar Kwankwaso ba – Abba Gida-gida

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Zababben Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa ba zai taba cin amanar mai gidansa kuma tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ba. Da ya ke jawabi ga magoya baya a Abuja, jim kadan bayan yanke hukuncin Kotun Koli da ta tabbatar masa da zabensa, Gwamna Yusuf ya nuna godiya ga Kwankwaso bisa kwazonsa na ganin cewa ba a zalunci al’ummar Kano ba. A cewar Gwamna Yusuf, “mu na godiya ga Allah da wannan gagarumar nasara da ya ba mu. Mu na kuma godiya ga jagoranmu, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bisa…
Read More