Editor

9513 Posts
Isra’ila Ta Jefa Bam Mai Nauyin Ton 2500 A Gaza – Jakadan Falasɗinu

Isra’ila Ta Jefa Bam Mai Nauyin Ton 2500 A Gaza – Jakadan Falasɗinu

Daga WAKILINMU Jakadan ƙasar Falasɗinu a Nijeriya, Abdullah Abu Shawesh, ya ce mamayar da ƙasar Isra’ila ta yi a Gaza ba komai bane illa ta yi shi da nufin aiwatra da kisan kiyashi. Shawesh ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya kira a ofishin jakadancin ƙasar na Nijeriya dake Abuja. Kazalika ya koka kan yadda ake kai hare-haren kan fararen hula babu ƙaƙƙautawa waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, da sunan ana yaƙar dakarun Hamas wanda duniya ta san ba haka ba ne. da yake buga misali kan irin rashin imanin da Isra’ila…
Read More
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Nasarawa inda ta tabbatar da nasarar Gwamna Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. A watan Oktoban da ya gabata ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a jihar ta soke nasarar Gwamna biyo bayan ƙarar da Jam'iyyar PDP a jihar da ɗan takarar Ombugadu suka shigar suna ƙalubalabtar sakamakon zaɓen. Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta ce ƙaramar kotun ƙarƙashin jagorancin Ezekiel Ajayi, ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke musamman wajen yin amfanin da bayanan shaidu ba bisa…
Read More
Shigar matasa a harkokin sarauta na ƙara dawo da martabar sarautun gargajiya – Giwar Matan Gona

Shigar matasa a harkokin sarauta na ƙara dawo da martabar sarautun gargajiya – Giwar Matan Gona

"Ina sa ran a siyasa na kai ga zama shugabar ƙasa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zainab Musa Ya'u, wata matashiya ce mai kimanin shekaru 22 da ta samu kai wa wani mataki na sarautar gargajiya da ba kasafai matasa masu ƙarancin shekaru irin nata suke samu ba. Rawar da take takawa a harkokin ƙungiyar raya al'adu da ɗaukaka kimar sarautun Ƙasar Hausa na Gamji Memorial Club a Jami'ar Jihar Gombe ya sa ta samun shiga a masarautar Gona da ke Ƙasar Akko, inda ta samu sarautar Giwar Matan Gona. A zantawar da ta yi da wakilin Blueprint Manhaja, Zainab ta…
Read More
Yanzu littafin ‘Turmin Danya’ ba na NNPC ba ne – Sulaiman Ibrahim Katsina

Yanzu littafin ‘Turmin Danya’ ba na NNPC ba ne – Sulaiman Ibrahim Katsina

Daga MUKHTAR YAKUBU Ga duk masu karatun littattafan Hausa shekaru 40 da suka wuce ba za su manta da littafin 'Turmin Danya' na Sulaiman Ibrahim Katsina ba, wanda ya zo na ɗaya a gasar da ma'aikatar kula da al'adu ta tarayyar Najeriya ta shirya a 1982. Kuma yana daya daga cikin littattafan da aka saka a cikin manhajar karatun gaba da firamare, don haka duk wani ɗan makaranta a wancan lokacin ya san da wannan littafin da ma sauran masu karatun Hausa. Don haka ne ma 'Turmin Ɗanya' ya shahara a wajen masu karatun Hausa da manazarta. Bayan tsawon shekaru,…
Read More
Wulaƙanci da rainin da marubuta ke fuskanta a Kano: laifin su waye?

Wulaƙanci da rainin da marubuta ke fuskanta a Kano: laifin su waye?

"Marubuta su ne masu yasa a rijiyar da ake shayar da al'umma ruwa don a rayu" Daga MUHAMMAD TAJAJJINI TIJJANI Marubuta na daga cikin mutane masu hankali, kaifin basira da zurfin tunanin da suka fi kowa muhinmmanci a cikin al'umma, amma a yanzu su aka fi kowa rainawa a fagen gudanar da al'amuran jama'a a nan Kano da ma wasu jihohin a Arewacin Najeriya. Kama daga ɗaiɗaikun mutane, ƙungiyoyi, ma'aikatu, masana'antu, makarantu kai har ma da uwa uba a gwamnati. Da yawa za ka ga ba su ɗauki marubuta komai ba. Ko menene dalilin da ya sa haka? Dalilin da…
Read More
Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Daga BASHIR ISAH Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya garzaya Kotun Ƙoli domin ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na soke nasarar da ya samu a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Kano. Wannan wata alama ce mai nuni da Gwamna Abba ba zai bari ya yi ƙasa a gwiwa bs wajen kare kujerarsa a matsayin Gwamnan Kano. Haka nan, wannan shi ne matakin kotu na ƙarshe da Yusuf zai ɗauka don kare kujerar tasa. Kwannan ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe, inda ta sauke Gwamna Abba na Jam'iyyar NNPP daga kujerar gwamnan Kano tare da…
Read More
Wa ke da alhakin tarbiyyar matasa a makarantu ne?

Wa ke da alhakin tarbiyyar matasa a makarantu ne?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A makon da ya gabata wasu rahotanni masu ɗaga hankali sun fito daga Jihar Taraba, inda aka rawaito wani ɗalibi ya daɓa wa malaminsa wuƙa a ciki, wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa. Washegarin ranar da wancan al'amari ya faru kuma wani ɗalibin Jami'ar Jihar Taraba ya yanka wani ɗalibi ɗan uwansa a wuya, wanda shi ma ya yi dalilin mutuwarsa. Duk a cikin wannan makon, wasu hotuna marasa daɗin gani sun fito daga wannan jihar dai, inda ake nuna wasu ɗalibai mata da suka kammala samun Diploma a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Taraba da…
Read More
Martin Cooper: Wanda fara ƙirƙiro wayar salula

Martin Cooper: Wanda fara ƙirƙiro wayar salula

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babu shakka batun wayar salula abu ne da ya dabaibaye duniya a halin yanzu. Da dai kafin zuwan wayar Salula, mutane suna rayuwarsu ne hankalin su a kwance, amma yanzu da wayar Salula ta zama ruwan-dare game duniya, babu wanda ya ke so ya rayu ba tare da ita ba. To shin zargi za mu yi ko kuma godiya ga wanda ya ƙirƙiro mana da wannan abu, wanda ya ke cinye wa mutane kuɗi? To imma dai zargin ne ko kuma yabon, to wanda za a zarga ko kuma a yaba shi ne Dakta Martin Cooper.…
Read More
Gwamna Lawal ya kama hanyar farfaɗo da martabar ilimi a Zamfara

Gwamna Lawal ya kama hanyar farfaɗo da martabar ilimi a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sha alwashin gwamnatinsa za ta maido da martabar ilimi a jihar. Ya bada wannan tabbacin ne a wajen taron ƙaddamar da aikin gyaran makarantun da suka lalace da kuma gina sabbi jihar. Sanarwar da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, Gwamnatin Jihar na bai wa ɓangaren ilimin jihar fifiko ne domin cika alƙawarin da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe. Sanarwar ta ƙara da cewa, fara aiwatar da wannan ƙudiri ya yi daidai da manufar ayyana Dokar ta Ɓaci a fannin ilimi jihar. Haka…
Read More
Kotu ta bada belin Emefiele kan N300m

Kotu ta bada belin Emefiele kan N300m

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a yankin Maitama a Abuja, ta bada belin tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele. Kotu ta bada belin nasa ne kan kuɗi Naira miliyan 300. Yayin zaman shari'a da kotun ta yi a ranar Laraba, Mai Shari'a Hamza Muazu ya buƙaci Emefiele da ya gabatar da shaidu guda biyu, kuma tilas shaidun ya zamana sun mallaki kadarori a yankin Maitama. Kodayake Emefiele bai halarci zaman kotun ba sakamakon yana tsare a gidan yarin Kuje tun a makon jiya. Kimanin makonni biyu da suka gabata wata Babbar Kotu a Abuja ta…
Read More