Editor

9513 Posts
Rigima ta ɓarke tsakanin matar jarumi Mista Ibu da ‘yarsa kan kuɗin tallafi da ya samu

Rigima ta ɓarke tsakanin matar jarumi Mista Ibu da ‘yarsa kan kuɗin tallafi da ya samu

Daga AISHA ASAS A daidai lokacin da shahararren jarumi a masana'antar fim ta Kudu, wato Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da Mista Ibu ke kwance gadon jinya tare da alhinin iftila'in da ya saukar masa, its kuwa maiɗakinsa mai suna Stella Maris, da kuma 'yarsa ta riqo Jasmine Okafor, suka fara nuna wa juna yatsa danganen da kuɗaɗen da abokanen sana'arsa da masoyansa na faɗin duniya suka yi tururuwar tura masa, sa'ilin da aka nemi taimakon jama'a don sama masa lafiya. Kamar yadda sanannen shafi a kafar sada zumunta ta Instagram, Gistlover, ya wallafa hoton firar 'yar ta…
Read More
Yadda bikin auren jaruma Rashida Maisa’a ya gudana

Yadda bikin auren jaruma Rashida Maisa’a ya gudana

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano A ranar Asabar ɗin da ta gabata, 11 ga Nuwamba, 2023 ne aka ɗaura auren jaruma a Kannywood Rashida Adamu Abdullahi Maisa'a, da angonta Alhaji Aliyu Adamu, Sardaunan Matasan Gwoza. An ɗaura dai a layin Malam Bello a Unguwar Daurawa, daura da babban Titin Maiduguri a cikin garin Kano, kuma an samu halartar jama'a masu yawa da suka shaida an ɗaura auren. Ita dai Rashida Adamu Abdullahi ba ta shirya wani taron shagulgulan biki ba, kamar yadda jaruman fim suka saba yi. An dai tara malamai a gidanta inda suka wuni suna karatun Alƙur'ani mai…
Read More
Al’ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa kan gwamnatina, cewar Gwamna Lawal

Al’ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa kan gwamnatina, cewar Gwamna Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya ce yana da yaƙinin al'ummar Zamfara na da ƙwarin gwiwa game da gwamnatinsa. Lawal ya samu tabbacin hakan ne ganin yadda masoyansa a birnin Gusau suka fito don tarbarsa bayan da ya dawo daga ziyarar aiki a ranar Litinin. Sanarwar da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce bisa la'akari da irin dandazon jama'ar da suka tarbi Mai Girma Gwamna, hakan manuniya ce game da ƙwarin gwiwar da al'ummar jihar ke da shi a kan gwamnatin jihar. A cewarsa, gwamnatin Gwamna Lawal ta samu soyayyar al'ummar jihar waɗanda…
Read More
Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna kaɗuwarsa bisa rasuwar fitaccen daraktan finafinan Hausa na Kannywood, Aminu S. Bono. Gwamna Abba ya bayyana hakan ne ta bakin Babban Sakataren Hukumar Tace Adabi na Jihar Kano, Abba El-Mustapha, wanda ya wakilce shi a wajen jana’aizar marigayin da aka gudanar ranar Talata, 21 ga Nuwamba, 2023, a maƙabartar Dandolo da ke birnin Kano. A ganawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala jana’izar, Abba ya kuma bayyana Marigayi Bono a matsayin mutumin ƙwarai mai haƙuri da yakana tare da kyakkyawar mu’amula, wanda kuma ya kai ƙololuwa wajen fikira…
Read More
Babban Hafsan Tsaro bai mutu ba, yana cikin ƙoshin lafiya – Hedikwatar Tsaro

Babban Hafsan Tsaro bai mutu ba, yana cikin ƙoshin lafiya – Hedikwatar Tsaro

Daga BASHIR ISAH Hedikwatar Tsaro da ke Abuja ta ƙaryata rahoton da ya ce Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya kwanta dama. Da safiyar wannan Talatar wasu jaridu suka yaɗa rahoto kan cewa, Musa ya rasu. Sai dai a martanin da ta mayar ta shafinta na X, Hedikwatar Tsaron ta ce rahoton ba gaskiya ba ne, don kuwa Babban Hafsan na raye kuma cikin ƙoshin lafiya. “Saɓanin wani rahoton ƙarya da aka yaɗa, Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa, yana nan a raye kuma cikin ƙoshin lafiya," in ji Hedikwatar. Sanarwar ta ƙara da cewa, jama'a su zamo…
Read More
Shugabannin tsaro sun bayyana gaban Majalisar Wakilai

Shugabannin tsaro sun bayyana gaban Majalisar Wakilai

Daga BASHIR ISAH Shugabannin fannin tsaro da Sufeto Janar na 'Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, sun bayyana a gaban Majalisar Wakilai domin tafka muhawara. Jami'an sun haɗa da Shugaban Tsaro (CDS), Janar Christopher Musa; Shugaban Rundunar Sojoji (COAS), Laftanal-Janar Taoreed Lagbaja; Shugaban Sojin Sama (CAS), Air Marshal Hassan Abubakar da kuma Shugaban Sojin Ruwa (CNS), Vice Admiral Emmanuel Ogalla. Wannan na zuwa ne biyo bayan caccakar da jami'an suka sha daga 'yan majalisar a makon jiya na tura wakilai da suka yi maimakon zuwa da-kai. A makon da ya gabata 'yan majalisar suka murtuƙe fuska na rashin zuwa zauren majalisar…
Read More
IPAC ta yaba wa gwamna Sule dangane da ayyukan cigaba a Nasarawa

IPAC ta yaba wa gwamna Sule dangane da ayyukan cigaba a Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Wata ƙungiyar haɗakar jam’iyyun siyasa mai zaman kanta da ake kira 'Inter-party advisory committee' wato IPAC a Turance na ƙasa ta yaba wa Gwamnan Jihar Nasarwa Injiniya Abdullahi Sule dangane da muhimman ayyukan cigaba da gwamnatin sa ke gudanarwa a jihar kawo yanzu. Shugaban kwamitin IPAC ɗin Yabati Sani ne ya bayyana haka wa manema labarai a lokacin wani ziyarar duba ayuka na musamman da ƙungiyar ke gudanar a duka jihohin ƙasar nan wadda ta faro da jihar ta Nasarawa. Ya ce ba shakka ayayin ziyarar duba ayyukan tawagar tasu ta gano wasu muhimman…
Read More
Rasuwar Aminu Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje

Rasuwar Aminu Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje

Da BASHIR ISAH Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana rasuwar Darakta a Kannywood, Aminu Surajo Bono, a matsayin babban rashi ga masa'antar fina-finai. Ganduje ya bayyana kaduwarsa game da rasuwar marigayin, inda ya ce mutuwar tasa ta zo a daidai lokacin da aka fi bukatar marigayin. Sanarwar da Sakataren Yada Labarai ga Ganduje, Edwin Olofu, ya sanya wa hannu wadda aka kuma aka raba wa manema labarai a ranar Talata ta ce, “Bono ya yi wa takwarorinsa zarra wajen bada hima da kuma yada al'adun Hausa/Fulani”. Sanarwar ta kara da cewa, a halin rayuwarsa, marigayin…
Read More
Ko amfani da kayan ƙarin ni’ima na haifar da ciwon sanyi?

Ko amfani da kayan ƙarin ni’ima na haifar da ciwon sanyi?

Daga AISHA ASAS A 'yan kwanakin baya mun yi darasi mai tsayi da ya shafi ciwon sanyi, abinda ke kawo shi, ma'anar sa, alamomi da sauransu. Kuma a taƙaice mun faɗa cewa, tushe-tushe, ko saka wasu abubuwa a farji da sunan gyara na iya zama silar gayyatar ciwon sanyi. A wannan satin za mu buɗe wannan darasi da amsa tambayar alaƙar da ke tsakanin kayan mata, ko ince hakin maye ko magungunan ƙarin ni'ima da ciwon sanyi. Idan mun soma da ainahin kayan da ake haɗawa da sunan ƙarawa mace ni'ima, za mu tarar ababe ne da suka haɗa ababe…
Read More
Kowa ya zarce a zaɓen gwamnan Bayelsa, Imo da Kogi

Kowa ya zarce a zaɓen gwamnan Bayelsa, Imo da Kogi

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Haƙiƙa zaɓen da ya gudana a ƙarshen mako ya zama zarcewa da kowace jam'iyya da ke kan gado a jihohin. Gabanin shiga zaɓen, mun yi bayani a makon jiya na yadda a ka fara har jihohi 7 su ka zama waje da sauran jihohi a lokacin gudanar da babban zave. Sakamakon shari'un kotu su ka sauya lokutan zaɓen jihohin. Yanzu ma ba abun mamaki ba ne waɗanda ba su gamsu da sakamakon zaɓen ba su sake garzayawa kotu don neman a yi sabon lale. Nan gaba ma akwai zaɓen gwamnan jihar Edo da Ondo. Abun…
Read More