Editor

9513 Posts
Gwamna Dauda Lawal ya yi zagayen duba aiki

Gwamna Dauda Lawal ya yi zagayen duba aiki

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kai ziyarar gani da ido a aikin hanyoyi da ake yi a Gusau, Babban Birnin Jihar. Aikin yana daga wani ɓangare na shirin bunƙasa birni da gwamnatin ta kawo, wanda kuma aka fara shi watan da ya gabata. Wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce gwamnan ya bayyana farin ciki da yanayin da aikin ke tafiya. Ya ƙara da cewa, a yayin ziyarar duba aikin hanyar, dandazon jama’a ne suka yi wa gwamnan tarba ta musamman. Ya ce: “A ranar 18 ga watan Agustan…
Read More
Hajjin 2024: NAHCON ta sanar da ƙarin kuɗin Hajji

Hajjin 2024: NAHCON ta sanar da ƙarin kuɗin Hajji

Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON), ta sanar da yiwuwar ƙarin kuɗin kujerar Hajji a yayin Hajjin 2024 idan Allah Ya kai mu. Hukumar ta ce Naira miliyan 4.5 shi ne mafi ƙarancin kuɗin da maniyyaci zai iya sakawa a asusun ajiya a ƙarƙashin hukumar wanda hakan ke nuni za a fuskanci ƙarin kuɗin kujerar Hajji a 2024. NAHCON ta ce ya zuwa yanzu tana nazarin rahotannin da kwamitoci suka gabatar mata dangane da Hajjin 2023 da ya gabata. Da yake jawabi a wajen taron manema labarai da hukumar ta shirya a Abuja, shugaban NAHCON na ƙasa, Zikrullah Kunle Hassan, ya…
Read More
Cancantar Yerima Shettima Yerima zama minista a gwamnatin Tinubu – Ƙungiya

Cancantar Yerima Shettima Yerima zama minista a gwamnatin Tinubu – Ƙungiya

Kiraye-kiraye ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan ya naɗa shugaban ƙungiyar matasan Arewa (AYCF), Yerima Shettima, a matsayin minista na ci gaba da samun tagomashi inda a yanzu ita ma ƙungiyar Progressive Young Leaders Assembly ta shiga sahun masu wannan ra'ayi. Shugaban ƙungiyar, Abubakar Kurawa, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar cewa naɗa Shettima muƙamin minista zai zama shaidar cewar Tinubu zai yi aiki tare da matasa s gwamnatinsa. A cewar ƙungiyar, "Mun lura da muhawarar da ake tafkawa kan buƙatar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta bai wa matasa damar riƙe muƙamin minista. "Mun fahimci…
Read More
Har yanzu ana kulle a aure? (2)

Har yanzu ana kulle a aure? (2)

Daga AMINA YUSUF ALI Barkanmu da shigowa wani sabon makon, masu karatu. Kada ku manta da batun da muke tattaunawa da ku a makon da ya gabata wato, kullen da ake yi wa matan aure. Wato yadda wasau mazan kan kulle matansu a gida su hana su fita kuma su hana su mua'amala da kowa. Mun faɗi ma'anar kulle da abubuwan da maza su yi don yin kulle. Mun faɗi guda biyar, hana ta mu'amala sosai da kowa har iyayenta, ƙwace wayarta, hana ta fita, hana ta sana'a, hana ta yin shigar da take so ko da ba ta saɓa…
Read More
Na sha tsangwama sanadiyyar tsumburewar jikina, har ya sa ni tunanin kashe kaina – Jarumi Aki

Na sha tsangwama sanadiyyar tsumburewar jikina, har ya sa ni tunanin kashe kaina – Jarumi Aki

Daga AISHA ASAS  A cikin wata tattaunawa da Chude Jideonwo, shahararren jarumin barkwanci da ya fito daga Jihar Abiya da ke Kudu maso Gabashin Najeriya, Chinedu Ikedieze, wanda aka fi sani da Aki, ya bayyana yadda tsayawar girman jikinsa ya zama babbar barazana ga walwalarsa tare da samun tsangwar da har ta sa shi tunanin ya kashe kansa ma ya huta. Jarumin ya bayyana cewa, saura ƙiris ya ɗauki ransa bayan da likita ya tabbatar wa mahaifiyarshi yana tare da laluran tsumburewar jiki, wanda hakan na nufin jikinsa ba zai ci gaba da girma daidai da shekarunsa ba. Jarumin ya…
Read More
Abba El-Mustapha ya yi rashin mahaifiya

Abba El-Mustapha ya yi rashin mahaifiya

Daga AISHA ASAS  Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, kuma tsohon jarumi a masana'artar Kannywood, Malam Abba El-Mustapha, ya yi rashin mahaifiyarshi mai suna Hajiya Aisha wadda ake kira da Gwaggo, a ranar Talatar da ta gabata. Sanarwar rasuwar wadda ta fito daga ɗan nata Abba El-Mustapha, yayin da ya wallafa a shafinsa na Facebook.  El-Mustapha ya bayyana rasuwar mahaifiyar tashi cikin jimami, tare da siffanta ta a matsayin rayuwarshi bakiɗaya.  “Na rasa mahaifiyata kuma duniyata, (Gwagwgo). Ya Allah ka jiƙan ta, ka gafarta mata kurakuranta, ka sa aljanna ce makomar ta. I will mourn you…
Read More
Manyan mutane nawa ke hannun jami’ai?

Manyan mutane nawa ke hannun jami’ai?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Gaskiya tun mutum na lissafawa har ya tsaya wajen gano yawan manyan mutanen da ke tsare a hannun jami’an tsaro don jiran ko a sake su ko a gurfanar da su a gaban kotu. Hakanan wasu kuma na gidan yari su na jiran yanke hukunci a caji daban-daban da su ke fuskanta. Abun da na ke nufi da manyan mutane su ne wadanda su ka shahara ko su ka tava riqe manyan muqaman gwamnati. Misali ma kafin na yi nisa a lokacin mulkin shugaba Buhari an yi ahuwa ga biyu daga manyan mutanen da a ka…
Read More
Shari’ar Zaɓen Shugaban Ƙasa: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci ma’aikata su zauna gida

Shari’ar Zaɓen Shugaban Ƙasa: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta umarci ma’aikata su zauna gida

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta umarci ma'aikata da su zauna a gida domin kallo da sauraren yadda za ta yanke hukunci kan ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa ya zuwa ranar Laraba, 6 ga Satumban 2023. Babban Akawun kotun, Oluwaleye Oluwasegun David, shi ne ya ba da sanarwar haka a ranar Litinin. Ɓangarori daban-daban ne suka shigar da ƙara inda suke ƙalubalantar nasarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata. A cewar David, iya waɗanda aka bai wa shaidar shiga za a bari su shiga harabar kotun ranar da kotun za ta yi zaman…
Read More
NLC a Neja ta ƙi amincewa da tallafin N110m da gwamnatin jihar ta ware mata

NLC a Neja ta ƙi amincewa da tallafin N110m da gwamnatin jihar ta ware mata

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) reshen Jihar Neja, ta ƙi amincewa da tallafin kuɗi Naira miliyan 110 da gwamnatin jihar ta ware mata, tana mai cewa a ƙara kuɗin cikin tallafin da gwamnati ta tanadar wa ma'aikatan jihar. Shugaban NLC na jihar, Comrade Abdulkarim Idris Lafene, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Litinin a Minna, babban birnin jihar. Lafene ya nuna ɓacin ran ƙungiyar ga gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Umar Bago saboda cire masu karɓar fansho daga tsarin rabon tallafin, lamarin da NLC ta ce bai zai saɓu ba. Shugaban ƙungiyar ya umarci ma'aikatan gwamnatin jihar…
Read More