19
Jul
Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin gaggawa kan sake fasalin rabon tallafin N8000 da yake shirin raba wa 'yan ƙasa sakamakon cire tallafin mai. Wannan umarni na ƙunshe ne cikin sanarwar da Tinibun ya fitar ranar Talata daddare ta bakin mashawarcinsa Dele Alake. Alake ya ce Tinubu ya sake ba da umarnin a bayyana wa 'yan Nijeriya tanadin da gwamnati ta yi don rage wa 'yan ƙasa raɗaɗin cire tallafin mai. Sanarwar ta ce Tinubu ya ba da umarnin waiwayar tallafin ne saboda yadda 'yan Nijeriya suka bayyana ra'ayoyinsu kan batun. A ranar 13…
