Editor

9513 Posts
Ƙungiyar masu gidajen burodi za su ƙara kuɗi a Nijeriya

Ƙungiyar masu gidajen burodi za su ƙara kuɗi a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Masu Gidajen Burodi a Nijeriya ta ce za ta ƙara farashin burodi da kashi 15 cikin ɗari daga ranar 24 ga watan Juli. A cikin wata sanarwa da ta fitar, bayan kammala taron shugabanninta na ƙasa, ƙungiyar ta 'Association of Master Bakers and Caterers of Nigeria' ta ce ta ɗauki matakin ne bayan la'akari da nunnukawar farashin kayan aiki. Sanarwar wadda ta samu sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Mansur Umar ta ce tashin farashin ya biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin Tarayya ta yi. A ranar 29 ga watan Mayun 2023…
Read More
Fitattun mawaƙan Nijeriya da suka taɓa zaman gidan kaso

Fitattun mawaƙan Nijeriya da suka taɓa zaman gidan kaso

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mun kawo wasu daga cikin mawaƙan da suka ɗanɗani zaman gidan yari da kuma dalilan da ya kai su. Sannan mun yi ma ku alƙawarin ci gaba da wannan darasi, don samun kawo ƙarin wasu kafin mu rufe darasin. Shahararrun mawaƙa da suka yi rayuwar gidan kaso na ɗan da dama, don haka ba za mu iya kawo wa masu karatu dukka ba, saboda haka za mu tsakuro ne daga ciki. A sha karatu lafiya. Burna Boy: Mawaƙi Burna Boy ba ya buƙatar gabatarwa a wannan zamani…
Read More
Tarihin Marigayi Yusuf Maitama Sule, Ɗan Masanin Kano

Tarihin Marigayi Yusuf Maitama Sule, Ɗan Masanin Kano

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sanin mutum sai Allah! Daga cikin mutane, akwai waɗanda Allah ke yi wa baiwar da bayyana ta ke da matuƙar wahala. Irin waɗannan mutane, rayuwarsu cike ta ke da darrusan da za a iya koya. Alhaji Yusuf Maitama Sule, Ɗanmasanin Kano, ɗaya ne daga cikin irin waɗannan mutane. Mutum ne mai ilimin addini da kuma na zamani. Allah ya yi masa baiwa da haƙuri, gaskiya, riƙon amana, cika alƙawari, sada zumunci, yafiya, barkwanci, dogaro da kai, da kuma sadaukar da kai. Mutum ne ɗan kishin ƙasa, mai son ganin jama’a sun ci gaba, mai son zaman…
Read More
Shugaba Tinubu ya dawo daga taron ƙasashen Afirka

Shugaba Tinubu ya dawo daga taron ƙasashen Afirka

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya dawo daga taron ƙungiyar ƙasashen Afrika (AU) da ya halarta a ƙasar Kenya. Bayanai daga birnin tarayya, Abuja, sun ce jirgin da ya dawo da Tinubu da tawagarsa ya sauka Babban Filin Jirgin Saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da misalin ƙarfe 4:20 na ranar Litinin. Manyan jami'an gwamnati ƙarƙashin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ne suka tarbi Tinubu a filin jirgin saman. Cikin waɗanda suka yi wa Tinubu rakiya har da Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila; Gwamnan Imo; Hope Uzodinnma da kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr…
Read More
Sojoji sun kama babbar mota ɗauke da alburusai da aka yi nufin kai su Anambra

Sojoji sun kama babbar mota ɗauke da alburusai da aka yi nufin kai su Anambra

Daga BASHIR ISAH Sojojin Nijeriya sun kama wata babbar motar ɗaukar kaya ɗauke da alburusai da nufin kai su Jihar Anambra. Rundunar sojin ta ce dakarun Bataliya ta 192 da ke yankin Dibishan 81 su ne suka kama motar ranar Asabar a daidai lokacin da aka yi amfani da ita wajen yin fasakwaurin alburusan. Rundunar ta ce an gano motar ce mai lamba ENU 697 XY a hanyar Ajilete-Owode cikin Ƙaramar Hukumar Yewa ta Arewa, Jihar Ogun, ɗauke da katan 720 na alburusai. Ga ƙarin hotuna:
Read More
Dandalin shawara: Mijina ba ya son haihuwa

Dandalin shawara: Mijina ba ya son haihuwa

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Salam. Ina wuni Asas. Allah Ya taimake ki ga dukan lamuranki. Ki taimake ni, yadda Allah ya taimake ki. Mijina da muka yi aure da shi shekara takwas. Da aka kawo ni gidanshi, kullum sai ya ba ni magani zai kusance ni, bai taɓa fashi ba, sai da na yi shakara biyu da aure, har shan maganin ya ishe ni, amma ko na yi ƙorafi sai ya rarashe ni, idan na ƙiya sai ya qi kusanta ta ko da kuwa ya matsu da son yi. To da iyaye suka fara zancen…
Read More
Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shuagaban Jam'iyyar APC na ƙasa da daga shiyyar Arewa, Abubakar Kyari, ya maye gurbin Sanata Abdullahi Adamu a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa biyo bayan murabus da Adamu ɗin ya yi. Wannan sauyin da jam'iyyar ta APC ta samu ya yi daidai da tanadin kundin dokokin jam'iyyar, wanda ya nuna cewa idan shugaban jam'iyyar na ƙasa ya yi murabus mataimakinsa ya maye gurbinsa a matsayin riƙon ƙwarya. An ga Kyari ya jagoranci mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam'iyyar wajen yin taro a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja cikin tsattsauran tsaro a ranar Litinin.…
Read More
Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Daga BASHIR ISAH Sbugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya miƙa wasiƙar yin murabus daga kujerarsa ta shugabancin jam'iyyar kamar yadda Jaridar News Point Nigeria ta rawaito. Majiyar News Point Nigeria ta bayya cewar, Sanata Adamu wanda ya zama shugaban APC a watan Maris, 2022, ya miƙa wasiƙar murabus daga muƙaminsa ga Fadar Shugaban Ƙasa gabanin dawowar Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ya halarta a ƙasar Kenya. Majiyar jaridar ta ce, Adamu ya aike da wasiƙar tasa ce ga Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, da misalin ƙarfe 4 na yammacin…
Read More
Talaka bawan Allah

Talaka bawan Allah

Tabbas a halin da ake ciki talakawa na cikin hali na gaba kura baya siyaki. Na ce talaka bawan Allah ba ina nufin ware ma su mulki da ma su wadata a cikin bayin Allah ba. Dukkanin mu bayinSa ne kuma wadata da talauci duka jarrabawa ce. Amma dai a wannan zamani amfi ganin damuwa ga ɓangaren talakawa a yanayi da mu ke ciki domin idan mutum bai da wadata hatta a gidansu zai zamo saniyar ware. Kai a matsayin mutum magidanci muddin bai da wadata ta a zo a gani hatta iyalai sai kaɗan ke zamowa ma su sauraren…
Read More
Buƙatuwar a dawo da kwalejojin horar da malamai

Buƙatuwar a dawo da kwalejojin horar da malamai

Akwai karin maganar Hausawa da ke cewa ‘kowa ya tuna bara, to bai ji daɗin bana ba.’ Mun kawo wannan karin magana ne saboda batun da mu ke son yin magana a kai, duk da mun taɓa dogon rubutu a kansa a watannin baya, wanda ya shafi harkar ilimi a ƙasar nan, musamman a nan Arewaci. A wancan rubutun mun kawo bayanai masu ilimantarwa game da yadda harkar ilimin Firamare ke neman taɓarɓarewa a Arewacin ƙasar nan, inda muka nuna cewa ba wani abu ba ne ya jawo haka illa watsi da gwamnatocinmu suka yi da Kwalejojin horar da Malamai,…
Read More