Editor

9513 Posts
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Everton na son ɗan wasan Faransa Moussa Dembele, mai shekara 27, da kuma mai bugawa Leicester, Jamie Vardy, mai shekara 36. Newcastle na ci gaba da tattaunawa da Leicester kan ɗan wasanta na gefe Harvey Barnes, mai shekara 25, kan fan miliyan £30. Ɗan wasan tsakiya a Nice da Wales Aaron Ramsey, mai shekara 32, ya samu tayi mai gwavi daga Saudiyya. Mai buga tsakiya a Tottenham da Denmark Pierre-Emile Hojbjerg, mai shekara 27, ya kasance matashin da Atletico Madrid ta jima tana zawarci. Chelsea a shirye take ta sayar da Trevoh Chalobah, mai shekara 24,…
Read More
Ahmed Musa ya jefa Ronaldo da Al-Nassr cikin matsala

Ahmed Musa ya jefa Ronaldo da Al-Nassr cikin matsala

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) ta haramta wa Al-Nassr rajistar sabbin ’yan wasa saboda rashin biyan wasu kuɗaɗen da Leicester City ke bin ta a wani ɓangare na yarjejeniyar Ahmed Musa. Al-Nassr ya sayi Cristiano Ronaldo ne a watan Janairun 2023 amma FIFA ta dakatar da ita daga sake yin rajistar sabbin ’yan wasa sakamakon taqaddama ƙungiyar Leicester. Hakan ya faru ne sakamakon gazawar kulob ɗin Saudiyyar na kasa biyan ƙungiyar Leicester ƙarin kuɗaɗe dangane da yarjejeniyar da ta yi da ɗan wasan Nijeriya, Ahmad Musa. Tsohon ɗan wasan gaban CSKA Moscow ya koma Foxes…
Read More
Wani sashe na kotu ya rufto wa Alƙalin-alƙalan Jihar Ekiti

Wani sashe na kotu ya rufto wa Alƙalin-alƙalan Jihar Ekiti

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Alƙalin-alƙalan Jihar Ekiti, Mai shari’a Oyewole Adeyeye, ya tsallake rijiya da baya a ranar Larabar da ta gabata, lokacin da wani sashe na babbar kotun jihar ya rufta masa a lokacin da yake ofishinsa. A yanzu dai mai shari’a Adeyeye yana samun kulawar likitoci a wani asibiti da ba a bayyana ba a jihar. Jaridar Manhaja ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a lokacin da yake bakin aiki ranar Laraba. Alƙalin dai yana ofishinsa ne a lokacin rugujewar. Wataqila lamarin ba zai rasa nasaba da giɓin tsarin da mamakon ruwan sama ya tsananta…
Read More
Discos na shirin ƙarin farashin wutar lantarki

Discos na shirin ƙarin farashin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Alamu masu ƙarfi na nuni da cewar akwai yiwuwar 'yan Nijeriya su fuskanci ƙarin kuɗin wutar lantarki nan ba da daɗewa ba. Hakan zai faru ne biyo bayan buƙatar da gamayyar kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) mai ƙunshe da kamfanoni 11 ta nuna kan ƙarin farashin lantarkin. Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ce ta bayyana haka a ranar Juma'a, 14 ga Yulin 2023. A cewar NERC, Gwamnatin Tarayya ta ce buƙatar sake duba farashin ta taso ne kan buƙatar haɗa sauye-sauye a ma’aunin tattalin arziki da sauran abubuwan da suka shafi ingancin sabis, ayyuka…
Read More
Tinubu ya ƙaddamar da shirin biyan Naira 8,000 ga magidanta miliyan 12

Tinubu ya ƙaddamar da shirin biyan Naira 8,000 ga magidanta miliyan 12

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da wani shiri na biyan Naira 8,000 na tsawon watanni shida ga iyalai miliyan 12 domin magance wahalhalun da ‘yan Nijeriya ke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur da aka yi. An bayyana hakan ne a cikin wata takarda da Kakakin Majalisar Wakilan Nijeriya, Tajudeen Abbas ya karanta a Zauren Majalisar a ranar Talata, 11 ga Yuli, 2023. Tinubu ya ce wannan tallafi ne domin baiwa talakawa da marasa galihu ‘yan Nijeriya damar shawo kan tsadar biyan buƙatu. Wasiƙar ta kasance ne don amincewa da ƙarin kuɗi…
Read More
Shehi Tijjani Sani Auwalun da na sani

Shehi Tijjani Sani Auwalun da na sani

Daga BILKISU YUSUF ALI Duk da tunanin wasu da ke mu’amala da siyasa daga nesa ba kasafai suke fahimtar kowanne al’amari ba musamman a lissafin S'siyasar shi ya sa wasu abubuwa kan ɗaure musu kai. Amma Wani jawabi da jagora Kwankwaso da ya yi sai na ƙara yarda da sakankacewar masu hange da tunanin Shehi Tijjani Sani Auwalu ba su san shi a Kumbotso ba lallai wancan lissafin na siyasa ya kufce musu. Akwai yan siyasar da suka yi yaƙi na sunkuru har Allah ya tabbatar da wannan kujerar ta Abba Wanda Shehu Tijjani yana ciki. Ba ma iya yaƙin…
Read More
Sojoji sun fatattaki ’yan bindiga a Filato

Sojoji sun fatattaki ’yan bindiga a Filato

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana cewa, dakarunta da aka aika garin Mangu ta Jihar Filato don magance rikicin da ke faruwa sun kashe wasu ’yan bindiga da dama. Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin ƙasa, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya wallafa a shafin rundunar na intanet ta ce, lamarin ya faru ne a Ƙaramar Hukumar Mangu mai fama da rikicin ƙabilanci ranar Laraba. Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan hukumomin jihar sun sanya dokar hana fita ta awa ashirin da hudu a Mangu bayan ɓarkewar rikici da ya yi sanadin mutuwar mutane…
Read More
Zargin tauye haƙƙi: Kotu ta yi watsi da ƙarar Kanu kan SSS

Zargin tauye haƙƙi: Kotu ta yi watsi da ƙarar Kanu kan SSS

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, Babban Birnin Tarayya, a ranar Alhamis, ta yi watsi da ƙarar da Nnamdi Kanu, Shugaban haramtacciyar ƙungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biyafar (IPOB), ya shigar a kan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS). Mai shari’a James Omotosho, a cikin hukuncin da ya yanke, ya ce, ƙarar Kanu ba ta da inganci kuma ya kamata a yi watsi da ita. Kanu, a ƙarar mai lamba: FHC/ABJ/CS/482/2022 da lauyansa ya shigar, ya maka Darakta Janar na DSS da Atoni-Janar na Tarayya, AGF, a matsayin masu amsa na 1 zuwa 3. A…
Read More
Kotu ta hana Gwamna Abba rushe wasu gine-gine a Kano

Kotu ta hana Gwamna Abba rushe wasu gine-gine a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Wata Babbar kotu ta hana Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Kabir Yusuf ci gaba da shirin rusa gidaje da ke kan titin BUK a Ƙaramar Hukumar Gwale ta jihar. Kotun ta amince da buƙatar da aka gabatar mata a ranar 4 ga watan Yuli, wanda Ibrahim Adamu, Lauyan masu ƙara a madadin Malam Bashir Abdullahi da wasu mutum 19 suka gabatar. Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Gwamna Abba Yusuf da babban lauyan gwamnati da kuma ofishin kula da filaye da tsare-tsare da raya biranen na Jihar Kano. Tuni dai Mai Shari’a Hafsat Yahaya-Sani,…
Read More
Kwararar Hamada: Gwanatin Tarayya ta dasa itatuwa sama da miliyan 10 a jihohi 11

Kwararar Hamada: Gwanatin Tarayya ta dasa itatuwa sama da miliyan 10 a jihohi 11

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau A ci gaba da ƙoƙarin da take yi na magance matsalar kwararowar hamada da ke addabar wasu jihohin ƙasar nan, Gwamnatin Tarayya ta hannun Hukumar Kula da Matsalar Hamada ta Ƙasa ta dasa itatuwa sama da miliyan 10 a jihohi 11 faɗin Nijeriya. Darakta Janar na Hukumar Kula da Kwararar Hamada, (NAGGW), Dokta Yusuf Maina Bukar ne ya bayyana haka a bikin zagayowar dashen itatuwa na shekarar 2023 a Gusau, babban birnin jihar ranar Alhamis. Dokta Bukar wanda ya samu wakilcin Daraktan Gudanarwa na hukumar, Nasiru Ismail, ya bayyana cewa, jahohi 11 da kwararar hamada…
Read More