Editor

9220 Posts
Gwamnatin Kano ta gano ma’ajiyar gurɓataccen taki da ake sayar wa manoma

Gwamnatin Kano ta gano ma’ajiyar gurɓataccen taki da ake sayar wa manoma

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta bankaɗo wata ma’ajiya da aka ajiye gurɓataccen taki a Gunduwawa da ke Ƙaramar Hukumar Gabasawa. Shugaban Hukumar Kare Haƙƙin mai Saye, CPC, Baffa Babba Ɗan’agundi ne ya bayyana hakan ta bakin mai magana da yawun hukumar, Musbahu Yakasai a ranar Laraba a Kano. “Mun samu bayanan sirri cewa akwai wani mamallakin ma’ajiyar taki yana haɗa takin da yashi, sannan ya siyarwa manoma. “Hakan ya sa muka ɗauki matakin rufe ma’ajiyar, domin kare al-ummar Jihar Kano daga amfani da taki maras kyau,” inji shi. Yakasai ya kuma ƙara da cewa a…
Read More
Harin jirgin ƙasa: Gwamnatin Buhari ta ci amanar talakawan Nijeriya – PDP

Harin jirgin ƙasa: Gwamnatin Buhari ta ci amanar talakawan Nijeriya – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa gwamnatin Muhammadu Buhari mai mulki ta ci amanar 'yan Nijeriya a tsawon mulkinta a ƙasar nan. Kakakin jam’iyyar Debo Ologunagba ya bayyana cewa, ”irin mulkin kama-karyar da APC take yi a ƙasar nan da kuma nuna halin ko-in-kula da take yi kan kiyaye rayukan mutanen ƙasar ya nuna gazawar gwamnatin. ”Ku duba yadda 'yan bindiga suke cin karensu ba babbaka a ƙasar nan. Duk wanda ya ga yadda 'yan bindiga ke jibgar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba sannan kuma gwamnati ta zuba musu ido,…
Read More
Kashi biyu cikin ɗari ne na ‘yan gudun hijira miliyan 3.2 aka yi rajistarsu, cewar gwamnati

Kashi biyu cikin ɗari ne na ‘yan gudun hijira miliyan 3.2 aka yi rajistarsu, cewar gwamnati

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Dubu tamanin da huɗu, da ɗari takwas da uku kacal, misalin kashi biyu cikin ɗari na miliyan uku da dubu ɗari biyu na ‘yan gudun hijira dake jibge a sassa daban-daban na ƙasar nan aka yi wa rajista ko hukuma ta san da zamansu, a cewar gwamnatin tarayya. Jihar Borno ita ce akan gaba da take da tarin ‘yan gudun hijira da suka kai kimani miliyan ɗaya da dubu ɗari shida, yayin da jihar Ekiti ke biye da ita da ‘yan gudin hijira dubu biyar da ɗari uku da saba’in da bakwai. Waɗannan bayanai sun…
Read More
Yadda ’yar Nijeriya, Tobi Amusan ta kafa tahiri a gasar tseren duniya

Yadda ’yar Nijeriya, Tobi Amusan ta kafa tahiri a gasar tseren duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tobi ’yar gaban goshin Nijeriya ce - BuhariYadda nasarar ta sa ’yan Nijeriya zubar da hawayen farin cikiKocin Super Eagles ya yaba wa Tobi da BrumeAfirika na alfahari da Tobi - Usain BoltShugaban Hukumar AFN ya taya ta murna 'Yan Nijeriya sun yi matuƙar farin cikin ganin yadda Tobi Amusan, 'yar shekara 25, haifaffiyar garin Ijebu Ode na Jihar Ogun, ta zama 'yar wasan Nijeriya ta farko da ta lashe kofin zinare a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya, bayan da ta samu nasara a gasar tseren mita 100 na mata a Oregon da ke ƙasar…
Read More
Aƙalla mutane miliyan uku za su shiga ƙangi kan shirin hana yanka jakuna a Nijeriya– Dillalai

Aƙalla mutane miliyan uku za su shiga ƙangi kan shirin hana yanka jakuna a Nijeriya– Dillalai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Dillalan Jakuna, DDA, ta ce shirin haramta yanka jakuna a ƙasar zai haifar da rasa ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya miliyan uku. Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Ifeanyi Dike ne ya bayyana hakan a wajen wani taron kwana ɗaya da aka gudanar kan wasu ƙudirori takwas na ɓangaren noma. Taron jin ra’ayin jama’a wanda ya gudana a ranar Litinin ɗin da ta gabata, kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin noma da raya karkara a ƙarƙashin Sanata Bima Enagi ya jagoranta. Ƙudirin dai mai suna: “Ƙudirin tabbatar da dokar yanka jaki da fitar da…
Read More
Badaƙalar Biliyan N109: Kotu ta bada belin Akanta-Janar, Ahmed Idris

Badaƙalar Biliyan N109: Kotu ta bada belin Akanta-Janar, Ahmed Idris

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Abuja mai zamanta a yankin Maitama, ta bada belin dakataccen Akanta-Janar na Ƙasa, Ahmed Idris. Idan za a iya tunawa, a ranar Juma'a kotu ta bada umarnin a garƙame Akanta-Janar ɗin tare da sauran waɗanda suke kare kansu a gidan yarin Kuje kafin sauraren buƙatar belin da suka shigar. A ranar 16 ga Mayun 2022 jami'an Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC) suka damƙe Idris bisa alaƙarsa da wawushe biliyan N80. Bayan 'yan kwanaki da kama shi ne sai Ministar Kuɗi da Tsare-tsaren Ƙasa, Zainab Ahmed, ta dakatar…
Read More
An rattaɓa hannu kan yarjejeniyar cinikayya da raya tattalin arziki ta Dalar Amurka miliyan 170 tsakanin Sin da ƙasashen Afirka

An rattaɓa hannu kan yarjejeniyar cinikayya da raya tattalin arziki ta Dalar Amurka miliyan 170 tsakanin Sin da ƙasashen Afirka

Daga CMG HAUSA A jiya Alhamis ne aka sanya hannu kan takardun haɗin gwiwa, da ayyukan raya tattalin arziki da cinikayya 14, tsakanin Sin da wasu ƙasashen Afirka da dama, waɗanda darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 170. An sanya hannu kan wadannan takardu ne a jiya Alhamis, yayin taron bunƙasa tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka, wanda ya gudana a birnin Changsha na lardin Hunan dake tsakiyar ƙasar Sin. Yarjejeniyoyin dai sun ƙunshi ɓangarorin haɗin gwiwar yankuna, da muhimman tsare-tsaren ayyuka, da samar da kuɗaɗen gudanarwa, da fannin hadin gwiwar zuba jari da cinikayya. Kazalika, a yayin…
Read More
Shin wane ne ya ɗanawa ƙasashen Afrika “tarkon bashi”?

Shin wane ne ya ɗanawa ƙasashen Afrika “tarkon bashi”?

Daga Fa’iza Mustapha Jaridar The Guardian ta Birtaniya, ya fitar da wani rahoto a baya-bayan nan, da ya yi kira ga cibiyoyin bayar da bashi na yammacin duniya, su sauƙaƙa tsarin biyan basussukan da suke bin ƙasashe masu karancin kuɗin shiga, musamman ƙasashen Afrika. Wannan rahoton na zuwa ne bayan cibiyar Debt Justice ta Birtaniyar, mai bibiyar yadda ake bayar da bashi tsakanin ƙasashen duniya, ta bankado wasu alƙaluma dake nuna cewa, basussukan da cibiyoyin kuɗi na yammacin duniya ke bin ƙasashen Afrika, ya rubanya wanda ƙasar Sin ke binsu har sau 3, haka kuma kuɗin ruwansu ya ninka na…
Read More
An tattauna tsakanin Shugaba Xi na Sin da Biden na Amurka

An tattauna tsakanin Shugaba Xi na Sin da Biden na Amurka

Daga CMG HAUSA Shugaban ƙasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden, inda suka tabo batutuwan da suka shafi dangantakarsu, da ma sauran batutuwan da suke da moriya iri guda. Tattaunawar ta gudana ne jiya Alhamis bisa roƙon shugaban Amurka, Joe Biden. Yayin tattaunawar, shugaba Xi Jinping ya ce duniya a yanzu na fuskantar matsaloli da sauye-sauye da giɓi wajen samun ci gaba da rashin tsaro dake karuwa. Ya ƙara da cewa, yayin da ake fuskantar sauye-sauye da tashin hankali, ƙasa da ƙasa da alummominsu a faɗin duniya, na sa ran Sin da…
Read More
An garƙame tsohon Akanta-Janar na Nijeriya, Ahmed Idris kan badaƙalar Naira biliyan 109

An garƙame tsohon Akanta-Janar na Nijeriya, Ahmed Idris kan badaƙalar Naira biliyan 109

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi An bayar da umarni a garƙame tsohon Akanta-Janar na Nijeriya, Ahmed Idris da wasu mutane biyu a gidan gyaran hali na Kuje dake Abuja, akan ha’inci ko zamba cikin aminci na zunzurutun kuɗaɗe na Naira biliyan 109. Babbar Kotu dake ƙarƙashin jagorancin Alƙali J.O. Adeyemi-Ajayi ita ce ta bayar da umarnin garƙame waɗannan mutane guda uku a ranar Juma’a da ta gabata lokacin da aka gurfanar da su bisa zargin yin zamba da halasta kuɗaɗen haram da ake tuhumar tsohon ma’ajin tarayyar ta Nijeriya. Alƙalin ya bayar da umarnin a garƙame su a kurkuku har…
Read More