30
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta bankaɗo wata ma’ajiya da aka ajiye gurɓataccen taki a Gunduwawa da ke Ƙaramar Hukumar Gabasawa. Shugaban Hukumar Kare Haƙƙin mai Saye, CPC, Baffa Babba Ɗan’agundi ne ya bayyana hakan ta bakin mai magana da yawun hukumar, Musbahu Yakasai a ranar Laraba a Kano. “Mun samu bayanan sirri cewa akwai wani mamallakin ma’ajiyar taki yana haɗa takin da yashi, sannan ya siyarwa manoma. “Hakan ya sa muka ɗauki matakin rufe ma’ajiyar, domin kare al-ummar Jihar Kano daga amfani da taki maras kyau,” inji shi. Yakasai ya kuma ƙara da cewa a…