07
Aug
’Yan Nijeriya na fama da ƙaranci da kuma tsananin tsadar burodi bayan masu gidajen burodi sun fara yajin aiki a faɗin ƙasar. A safiyar Alhamis ɗin makon da ya gabata ne Babbar Ƙungiyar Masu Gidajen Burodi ta fara yajin aiki, saboda abin da ta kira tashin gwauron zabon kayan haɗa burodi. Tun kafin fara yajin aikin nasu da zai ɗauki tsawon kwana huɗu, ’yan Nijeriya ke ta bayyana damuwa, bayan a wasu wuraren an ninka farashinsa. Shugaban Ƙungiyar Masu Gidajen Burodi da Dangoginsu ta Ƙasa, Emmanuel Onuorah tare da Kakakin ƙungiyar, Babalola Thomas sun buƙaci Gwamnatin Tarayya ta dakatar da…