Editor

9316 Posts
Ƙaranci da tsananin tsadar burodi a Nijeriya

Ƙaranci da tsananin tsadar burodi a Nijeriya

’Yan Nijeriya na fama da ƙaranci da kuma tsananin tsadar burodi bayan masu gidajen burodi sun fara yajin aiki a faɗin ƙasar. A safiyar Alhamis ɗin makon da ya gabata ne Babbar Ƙungiyar Masu Gidajen Burodi ta fara yajin aiki, saboda abin da ta kira tashin gwauron zabon kayan haɗa burodi. Tun kafin fara yajin aikin nasu da zai ɗauki tsawon kwana huɗu, ’yan Nijeriya ke ta bayyana damuwa, bayan a wasu wuraren an ninka farashinsa. Shugaban Ƙungiyar Masu Gidajen Burodi da Dangoginsu ta Ƙasa, Emmanuel Onuorah tare da Kakakin ƙungiyar, Babalola Thomas sun buƙaci Gwamnatin Tarayya ta dakatar da…
Read More
Tashin farashin baƙin mai da canji sun jawo min naƙasu a kasuwancina – Obasanjo

Tashin farashin baƙin mai da canji sun jawo min naƙasu a kasuwancina – Obasanjo

Daga AMINA YUSUF ALI Tsohon shugaban ƙasar Nijeriya a Jamhuriya ta biyu, Olusegun Obasanjo ya bayyana yadda tashin farashin baƙin mai da canji suke kawo masa naƙasu a kasuwancinsa. Shugaban ya ƙara da cewa, tashin farashin baƙin man yana da alaka da yadda ake gudanar da mulkin ƙasar nan ba yadda ya kamata ba. A cewar tsohon shugaban, tashin farashin yana jawo cikas sosai a kasuwancinsa na kifi. Mista Obasanjo wanda ya mallaki sashen kiwon kifi a gidansa dake Abeokuta ta jihar Ogun ya bayyana haka ga manema labarai a ranar Talatar da ta gabata a yayin taron ƙungiyar daidaita…
Read More
Akwai sauran mutanen jirgin ƙasan Abuja-Kaduna a daji

Akwai sauran mutanen jirgin ƙasan Abuja-Kaduna a daji

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Za a ji ana sako fasinjojin da ɓarayi su ka sace a harin jirgin ƙasa kan hanyar Abuja zuwa Kaduna tun ranar 28 ga watan Maris ɗin bana 2022 miladiyya, amma har yanzu akwai sauran mutane da ke dajin cikin matuƙar takaici da rashin sanin tabbas. Duk haka su din ma masu nisan kwana ne don lokacin mummunan farmakin fasinjoji 9 su ka gamu da ajali. A wannan lokacin ko ma rai bai yi halin sa ba, ko ba a sace mutum ba, akwai mummunan tashin hankali na rugugin harbin bindiga da firgita marar misali. Waɗanda…
Read More
Barazanar ambaliyar ruwa a Nijeriya

Barazanar ambaliyar ruwa a Nijeriya

A yayin da Tarayyar Nijeriya ke ci gaba da fuskantar barazanar ambaliya ruwa a sassa dabam-dabam, gwamnatin ƙasar ta ce ba ta da haufin ingancin madatsun ruwan da Nijeriyar ke da su. Kama daga tituna da gadoji da ma uwa uba gidajen al'umma dai, sannu a hankali ambaliyar ruwa na bazuwa a sassan Tarayyar Nijeriyar dabam-dabam. Kuma ya zuwa yanzu, kimanin jihohi 28 da ƙananan hukumomi 121 ne ambaliyar da ke yin barazana ta shafa a ƙasar. An fuskanci ambaliyar ruwa mafi muni a tarihin Nijeriya a shekarar 2012, inda aka yi asarar kusan dala biliyan 16.9. Daga cikin manufofin…
Read More
2023: INEC za ta yi amfani da dokokin zaɓe ba tare da tsoro ba – Yakubu

2023: INEC za ta yi amfani da dokokin zaɓe ba tare da tsoro ba – Yakubu

Daga SANI AHMMAD GIWA a AbujaHukuma Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, za ta yi taka-tsan-tsan wajen aiwatar da dokoki, musamman Dokar Zaɓe ta 2022, ba tare da tsoro ko son rai ba, don tabbatar da sahihin zaɓe, gaskiya da adalci a 2023. Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Laraba a Abuja, a wajen taron tunawa da Marigayi Darakta Janar na Cibiyar Zaɓe, TEI, Farfesa Abubakar Momoh, wanda ya rasu a ranar 29 ga Mayu, 2017. Mista Yakubu ya samu wakilcin Farfesa Abdullahi Zuru, kwamishinan ƙasa kuma shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa.…
Read More
Ba mu yanke shawarar barin APC ba, inji Ɗanmalikin Kabi

Ba mu yanke shawarar barin APC ba, inji Ɗanmalikin Kabi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Ƙungiyar nan mai rajin lalubo nagartattun shugabanni (Likemind Initiative For Good Governance) a ƙarƙashin jagorancin Alhaji Musa Abubakar Ɗanmalikin Kabi ta ce har yanzu ba ta yanke shawarar barin Jam'iyyar APC ko kuma ta tsayawa a cikinta ba har yanzu. Shugaban ƙungiyar na ƙasa Alhaji Musa Abubakar Ɗanmalikin Kabi ne ya bayyana haka bayan kammala wani taron masu ruwa da tsaki na wannan ƙungiyar da aka gudanar a ɗakin taro da ke Unity Hall a garin Birnin Kebbi ƙarshen makon da ya gabata. Alhaji Musa Abubakar Ɗanmalikin Kabi ya bayyana cewa tun shekarar 2015 da…
Read More
‘Yan sanda za su fara kai samame dazuka da gine-ginen da ba kowa a Abuja

‘Yan sanda za su fara kai samame dazuka da gine-ginen da ba kowa a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 'Yan sandan Birnin Tarayyar Nijeriya Abuja sun fara hai samame dazuzzuka da gine-ginen da babu kowa a cikin gari da unguwannin bayan gari. Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Josephine Adeh ne ya faɗi hakan a ranar Laraba, kamar yadda kafar yaɗa labaran Channel ta ruwaito. A yayin da take ƙaryata jita-jitar cewa akwai mafakar masu garkuwa da mutane a cikin Abuja, ta ce a kwanaki masu zuwa mazauna birnin za su ga an tsaurara matakan tsaro. Harin ya zo ne ƙasa da sa'a 24 ba bayan da rundunar 'yan sanda ta yi…
Read More
Magance matsalar tsaro ita ce kan gaba da zaɓen 2023, cewar Hashim

Magance matsalar tsaro ita ce kan gaba da zaɓen 2023, cewar Hashim

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Tsohon ɗan takarar neman shugabancin ƙasar nan, kuma jigo a Jam’iyyar APC dake jagorancin ƙasar nan, Mr. Gbenga Olawepo-Hashim ya roƙi shugabancin siyasar Nijeriya da kada su tara lissafe-lissafe da tunanin su kacokan akan zaɓen shekara ta 2023, a maimakon damuwar lamuran tsaro da suke da buqatar ɗaukar matakan gaggauwa, yana mai gargaɗin cewa: “Wajibi ne mu tabbatar da lafiyar zamantakewar jama’a, kafin waiwaitar lamuran gudanar da zaɓe, domin sai jama’a suna raye ne cikin kyakkyawan tsaro da ƙoshin lafiya sa’annan suke neman jefa ƙuri’ar zaɓe." Da yake gabatar da nasihar cewa, lamuran rashin tsaro…
Read More
Tsoffin ɗaliban Kwalejin Sa’adu Rimi na ‘yan ajin 92 sun yi taron cika shekara 30 da kammalawa

Tsoffin ɗaliban Kwalejin Sa’adu Rimi na ‘yan ajin 92 sun yi taron cika shekara 30 da kammalawa

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Tsofaffin ɗalibai na Kwalejin Ilimi ta Sa'adu Rimi da ke Kano Kano, 'yan ajin 1992 sun yi taron cika shekaru 30 da kammala makarantar. Taron wanda aka yi a ranar Lahadi a ɗakin taro dake harabar kwalejin ya samu halartar ɗimbin tsofaffin ɗaliban da wasu daga cikin malamai da suka koyar da su. Da yake bayani akan maƙasudin taron, shugaban riƙo na ƙungiyar, Mai Shari'a Kamilu mai Sikeli ya ce ƙungiyar ta samo asali ne daga gama makarantar saboda ba sa haɗuwa da juna sai in wani abu ya taso ko a ɗaurin aure ko…
Read More
Manufata ita ce haɓaka tattalin arzikin Jigawa nan da shekara 35 – Lamido

Manufata ita ce haɓaka tattalin arzikin Jigawa nan da shekara 35 – Lamido

Daga SANI AHMAD a Abuja Ɗan takarar gwamna a Jam'iyar PDP a Jihar Jigawa, Mustapha Sule Lamido ya ce yana da manufar inganta tattalin arzikin Jihar Jigawa a cikin shekara 35 masu zuwa idan aka zaɓe shi a matsayin gwamna. Mustapha, wanda ɗa ne ga tsohon gwamnan jihar Sule Lamido, ya ce dole ne su zauna da masu ruwa da tsaki a jihar domin tabbatar da wannan burin nasa idan har ya zama gwamnan. "Za mu haɗa kai da ƙwararru da sarakuna da malamai wajen samar da aiki ga matasa. "Muna so mu ɗora Jigawa akan tafarkin inganta ta a…
Read More