Editor

9313 Posts
Mun horas da matasa sama da 17,000 – Global Concept

Mun horas da matasa sama da 17,000 – Global Concept

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Cibiyar Horas da Matasa Sana'o'in Dogaro da kai daban-daban wace ke samun talafin daga gidauniyar Dr. Rufai Mukhtar Ɗanmaje foundation da sauran masu kishin aluma a kano da ƙasa baki ɗaya yanzu haka ta samu nasarar hurara da matasa sama da dubu 17 sanaoi daban daban kamar ɗaukar hoto koyar da kwamfuta, ɗinki, koyar da aikin jarida da sauran sana`o'i. Wannan bayani ya fito ne daga bakin Kwamared Mukhtar Musa 'Yankaba, babban jami'i mai kula da cibiyar a lokacin da yake jawabi yayin bikin yaye wasu ɗalibai kimanin 200 da wani bawan Allah ya ɗauki…
Read More
Jama’a ku daina ganin laifin Buhari da Ganduje – Madugawa

Jama’a ku daina ganin laifin Buhari da Ganduje – Madugawa

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Alhaji Salisu Madugawa, dattijo ɗan shekara 72 a duniya kuma shugaban Ƙungiyar Manoma ta Amana Farmers Association ta Ƙasa, reshen Jihar Kano, ya bayyana cewa cigaban Kano da aka samu a zamanin Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje da kuma wasu matsaloli na rayuwa da ake samu dama haka rayuwa take akwai nasara akwai ƙalubale, don haka bai kamata mutanen Kano su riƙa maganganu ko ganin matsalar gwamnan Kano ba domin shi ɗan Adam ne zai iya yin daidai zai kuma iya yin akasin haka; don haka zage-zage ko maganganu marasa kan gado a cewarsa bai…
Read More
‘Yan sanda na bincike kan budurwar da ta rataye kanta a Kano

‘Yan sanda na bincike kan budurwar da ta rataye kanta a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kano tana ci gaba da bincike kan abin da ya sa wata budurwa mai shekara 17 ta rataye kanta a ƙauyen Garin Dau da ke yankin ƙaramar hukumar Warawa. Mafi akasarin mazauna ƙauyen dai sun yi zargin cewar budurwar ta rataye kan nata ne bisa auren dole da iyayenta ke shirin yi mata. Sai dai iyayen nata sun musanta wannan zargi inda suka ce ba ta kammala makarantar sakandare ba, balle a yi maganar aurar da ita. Faruwar wannan lamari dai ya zo wa mazauna yankin da mamaki, sakamakon yadda…
Read More
An damƙe ɗan sandan da ake zargi da karɓar na-goro a Edo

An damƙe ɗan sandan da ake zargi da karɓar na-goro a Edo

Daga BASHIR ISAH Rundunar 'Yan Sandan Jihar Edo ta damke jami'inta, Kwanstebul Victor Osabuohign, wanda aka yada bidiyonsa a kafafen sada zumunta yana karɓar cin hanci. Mataimakiyar Jami'in Hulɗa da Jama'a na rundunar, ASP Jennifer Iwegbu ce ta ba da sanarwar hakan ranar Juma'a a Benin, babban birnin jihar. An ga Osabuohign cikin wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta yana cinikin abin da za a ba shi a matsayin na-goro da wani matafiyi mai suna Arc. Bolu. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya rawaito cewa, Iwegbu ta ce an kama jami'in da lamarin ya shafa kuma ana…
Read More
Shugaban APC ya gargaɗi masu tayar da zaune tsaye a yankin Abia

Shugaban APC ya gargaɗi masu tayar da zaune tsaye a yankin Abia

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Adamu, ya bayyana baƙin cikinsa kan rashin haɗin kai a jam’iyyar reshen Jihar Abia, yana mai cewa rikicin ya fi na sauran jihohi ƙamari. Adamu wanda ya yi magana a wani taro da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC na Abia a Abuja, ya caccaki tsohon ƙaramin ministan ma’adanai na ƙasa, Mista Uche Ogah, kan zarginsa da hannu a rikicin da ya ɓarke. An ce ya nuna rashin jin daɗinsa da Ogah bisa zarginsa da jagorantar wata ƙungiyar da ke adawa da juna a cikin jam’iyyar APC ta jihar…
Read More
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin ta aike da sammaci ga wasu jakadun ƙasashen turai da ƙungiyar EU don nuna rashin jin daɗinta

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin ta aike da sammaci ga wasu jakadun ƙasashen turai da ƙungiyar EU don nuna rashin jin daɗinta

Daga CMG HAUSA Jiya ne, mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Sin Deng Li ya aike da sammaci ga wasu jakadun ƙasashen Turai da ƙungiyar EU da ke ƙasar Sin, don nuna rashin jin daɗinta kan yadda ministan harkokin wajen ƙasashe mambobin ƙungiyar G7 da babban wakilin ƙungiyar EU mai kula da harkokin diplomasiyya da tsaro suka bayar da sanarwar nuna halin ko-in-kula kan batun yankin Taiwan na ƙasar Sin. Deng ya bayyana cewa, sanarar da ministocin ƙasashen ƙungiyar G7 da kuma babban wakilin suka bayar, sun jirkita haƙiƙanin shaidu, wadanda suka mayar da fari baki. Wannan tamkar tsoma baki ne…
Read More
Jami’an Amurka na zuzuta batun tarkon bashi ne domin haddasa rigima

Jami’an Amurka na zuzuta batun tarkon bashi ne domin haddasa rigima

Daga CMG HAUSA Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Hua Chunying, ta ce abun da ake kira da tarkon bashi na ƙasar Sin, abu ne da aka shirya. Kuma ko dangantakar Sin da Afrika na da kyau ko a’a, ƙasashen Afrika ne suke da abun cewa akai. Don haka, ba hurumin Amurka ba ne, jayayya da batun ko haddasa fitina da yada jita-jita don shafawa abotar Sin da Afrika baƙin fenti. Hua Chunying ta bayyana haka ne yayin taron manema labarai na yau Alhamis, inda take mayar da martani kan zuzuta maganar da na tarkon bashi da jami’an Amurka ke yi…
Read More
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin ta sanar da matakan martani ga ziyarar da Pelosi ta kai Taiwan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin ta sanar da matakan martani ga ziyarar da Pelosi ta kai Taiwan

Daga CMG HAUSA A yau Alhamis, ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Sin, ta sanar da cewa za a soke shirin da aka yi na wayar tarho tsakanin kwamandojin rundunonin sojin ƙasashen Amurka da Sin da kuma ganawar da za a yi tsakanin ma’aikatunsu na tsaro, tare da sauran wasu matakai. Haka zalika, ƙasar Sin ta yanke shawarar ƙaƙaba wa Pelosi tare da iyalanta takunkuman da suka dace da tanadin dokokin jamhuriyar jama’ar ƙasar Sin. Wannan matakin martani ne da Sin ta ɗauka, saboda nacewar da kakakin majalisar wakilan Amurka ta yi, wajen ziyartar yankin Taiwan, duk da adawa da korafin da…
Read More
Rundunar Sojan Nijeriya ta soma bincike kan kisan ɗan sanda a Legas

Rundunar Sojan Nijeriya ta soma bincike kan kisan ɗan sanda a Legas

Daga BASHIR ISAH Rundunar Sojan Nijeriya ta kafa kwamitin musamman don gudanar da bincike kan matuwar wani ɗan sanda da ake zargin soja ne ya kashe shi yayin rashin jituwar da aka samu tsakanin 'yan sanda da sojoji a Legas. Muƙaddashin Mataimakin Daraktan Sashen Hulɗa da Jama'a na 81 Division, Manjo Olaniyi Osoba ne ya tabbatar da hakan cikin sanarwar da aka raba wa manema labarai ranar Juma'a. Manjo Osoba ya yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta'aziyyar Rundunar Sojan Nijeriya ga iyalan marigayin, tare da ba da tabbacin rundunar za ta yi bincike domin gano haƙiƙanin gaskiyar abin…
Read More