12
Mar
Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya taimaka ya sake buɗe iyakokin ƙasa don shigowa da kayan abinci wanda a cewarsa, hakan zai taimaka wajen daƙile ƙarancin abincin da ake fama da shi a ƙasa. Wannan kira na ƙunshe ne cikin sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa, wadda aka fitar jim kaɗan bayan da Gwamnan ya karɓi baƙuncin Kwantrola Janar na Hukumar Fasa-ƙwauri ta Ƙasa, Bashir Adewale Adeniyi, a Fadarr Gwamnatin Jihar da ke Kano. Gwamna Yusuf ya koka kan yunwar da ake…
