Editor

9513 Posts
Ba dalilin da zai sa ka ƙaro aure alhali gidanka bai ƙoshi ba – Nafisa Usman

Ba dalilin da zai sa ka ƙaro aure alhali gidanka bai ƙoshi ba – Nafisa Usman

"idan ba ki da haƙuri ba za ki iya samun kwangila a gwamnati ba" Daga AISHA ASAS Mace halitta ce da aka halita da wata baiwa ta musamman da ba kasafai ake samunta a maza ba, wato baiwar iya yin ababe da dama a lokaci guda. Ma’ana dai mace za ta iya aikin kula da kanta, iyalinta kuma ta samu iya neman kai ba tare da ɗaya ya samu rauni ba. Haka kuma mace za ta iya yin ayyuka da dama da ake ganin ƙarfin ƙwaƙwalwarta da ƙwazonta bai kai ba. A wannan makon shafin Gimbiya ya ɗauko maku matar…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Nijeriya ta buɗe iyakokinta da Nijar

Da Ɗumi-ɗumi: Nijeriya ta buɗe iyakokinta da Nijar

*Ta janye mata ragowar takunkumai Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bada umarnin gaggawa kan sake buɗe iyakokin Nijeriya da Nijar ta ƙasa da sama, tare da ɗage sauran takunkuman da aka ƙaƙaba wa ƙasar. Mai magana da yawun Shugaba Ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka a ranar Laraba. Sanarwar ta ce hakan ya yi daidai da umarnin ECOWAS wanda ta bayar yayin taron da ta yi ranar 24 ga Fabrairu a Abuja. A cewar sanarwar, “Shugabanni ECOWAS sun amince a kan janye takunkuman da aka kafa wa Jamhuriyyar Nijar, Mali, Burkina Faso da kuma Guinea. “Shugaban Ƙasa ya ba…
Read More
Yadda za mu dawo da ɗabi’ar karatun littafi

Yadda za mu dawo da ɗabi’ar karatun littafi

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A ƙarshen makon da ya gabata ne, na samu gayyata daga wata cibiya mai kula da ilimin matasa a fannonin ilimi daban-daban a matakin gaba da sakandire, mai suna Majema College of Advanced Studies Jos, wacce ta karrama ni daga cikin jerin mutanen da ta zaɓa don yabawa ƙoƙarin da suke yi wajen ba da gudunmawa a harkokin ilimi da rayuwa. Wannan karramawa da na samu a cikin jerin manyan mutanen da aka zaɓo daga ɓangaren malaman addini da na boko, ’yan kasuwa, 'yan siyasa da kuma ’yan jarida, ta yi matuƙar birgeni, musamman ganin cewa…
Read More
Mulkin soja

Mulkin soja

Daga AMINA YUSUF ALI Idan ka ji mutum yana fatan mulkin soja a Nijeriya, to cikin biyu ɗaya ne; ko dai yaro ɗan 90's wanda bai san mene ne mulkin soja ba, ko kuma babban wanda bai san ciwon kansa ba. Waɗannan su ne suke fatan sojoji su yi juyin mulkin a Nijeriya. Duk wanda ya san mulkin soja, to ba zai yi fatan sojoji su karvi ragamar ƙasar nan ba a halin da ake. Ko ni nan da aka haifa a zamanin mulkin Abacha, ruwan zafin da ake mini wanka da shi daban yake da na waɗanda da aka…
Read More
Jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Ya sha alwashin bunƙasa harkokin finafinai Daga BASHIR ISAH Jarumi a masana'antar Kannywood, Dokta Ali Nuhu, ya kama aiki a hukumance a matsayin Shugaban Hukumar Fina-finai ta Ƙasa (NFC). Sanarwa mai ɗauke da sa hannun Daraktan Hulɗa da Jama'a na hukumar, Brian Etuk, ta nuna a ranar Talata Ali Nuhu ya shiga ofis a matsayin shugaban hukumar na bakwai. Ta ƙara da cewa, jarumin ya sha alwashin yin aiki tukuru don bunƙasa masana'antar fina-finai ta Nijeriya. Da yake jawabi a wajen bikin karɓar ragamar aiki wanda aka shirya a hedikwatar hukumar da ke Jos, babban birnin Jihar Filato, Ali Nuhu…
Read More
‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Kaduna sun ce aƙalla mutum 61 wasu da ake zargin 'yan fashin daji ne suka yi garkuwa da su a yankin Buda da ke cikin Ƙaramar Hukumar Kajuru a jihar. Duk da dai babu bayani a hukumance ka aukuwar harin, sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa majiyarmu ranar Talata cewar, maharan sun dira ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:45 na dare inda suka yi awon gaba da mutum 61. A cewar Dauda Kajuru wanda mazaunin yankin ne, 'yan bindigar shiga yankin da yawansu, kuma sun harba bindiga. Ta bakinsa, “abin da ya…
Read More
Yanzu-yanzu: Majalisar Dattawa ta dakatar da Ningi na wata uku kan zargin cushen kasafi

Yanzu-yanzu: Majalisar Dattawa ta dakatar da Ningi na wata uku kan zargin cushen kasafi

Majailisar Dattawa ƙarƙashin jagorancin Sanata Godswill Akpabio, ta dakatar da Sanata Abdul Ningi na tsawon wata uku daga majalisar. Manlisar ta ɗauki wannan mataki ne yayin zaman da ta yi ranar Talata, kuma ta dakatar da Ningi ne bayan da ya yi zargin an yi cushe na Naira tiriliyan 3.7 cikin Kasafin 2024. A wata hira da BBC Hausa ta yi da ɗan majalisar mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya kwanan nan, aka ji shi ya ce haƙiƙanin kasadin 2024 da aka gabatar Tiriliyan 25 amma ba Tiriliyan 28 da ake amfani da shi a halin yanzu ba. Ya ce bayan…
Read More
Ana fargabar yara biyu sun mutu sakamakon gobara a sansanin ‘yan gudun hijira a Borno

Ana fargabar yara biyu sun mutu sakamakon gobara a sansanin ‘yan gudun hijira a Borno

Bayanan da MANHAJA ta kalato daga Jihar Borno a wannan Talatar sun ce, an samu aukuwar gobara a Sansanin 'Yan Gudun Hijira da ke yankin Muna a Maiduguri a jihar. Duk da dai babu wani bayani a hukumance, amma wasu majiyoyi sun ce gobarar ta yi ajalin wasu yara guda biyu. Har zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton, ba a kai ga gano dalilin da ya haifar da gobarar ba. Haka nan, 'yan sanda a jihar ko gwamnati, babu wanda ya ce uffan kan lamarin kawo yanzu. Jihar Borno na daga cikin yankun da suke fama da hare-haren Boko Haram…
Read More
Makaɗin Hausa: Marigayi Alhaji Sa’idu Mai Daji Sabon-Birni

Makaɗin Hausa: Marigayi Alhaji Sa’idu Mai Daji Sabon-Birni

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Alhaji Sa’idu Mai Daji a garin Tara ta sarkin Kwanni, ita kuma Tara tana bin Sabon-Birni ta sarkin Gobir, jihar Sakkwato. Sannan mahaifinsa shi ne Mainasara. Ya kiyasta cewa yana da shekara arba’in da biyar (45), watau ke nan an haife shi a wajejen 1938. Dalilin kiransa Maidaji shi ne, a lokacin rayuwar mahaifinsa suna zaune ne a tsohon garin Tara. Sai wata rigima da faɗace-faɗace ta haddasu tsakanin mutanen Tarar, sai aka yi ta tashi ana barin garin, bayan kuwa har sun yi shuka. Mahaifinsa Mainasara, ya ce shi kam ba zai bar…
Read More
Birtaniya ta haramta wa likitoci ‘yan Nijeriya masu aiki a ƙasar zuwa da ‘yan uwansu

Birtaniya ta haramta wa likitoci ‘yan Nijeriya masu aiki a ƙasar zuwa da ‘yan uwansu

Daga BASHIR ISAH Ƙasar Birtaniya ta haramta wa ma’aikatan kiwon lafiya a ƙasar zuwa da 'yan uwansu ƙasar. Ofishin cikin gida na Birtaniya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin. Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne a matsayin ɓangare na ƙoƙarin da Gwamnatin ƙasar ke yi wajen yaƙi da matsalar shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba. Ta ƙara da cewa a bara kaɗai, jimillar ma'aikata 120,000 ne suka raka ma'aikata 100,000 zuwa Birtaniya. "Masu ba da kulawa a Ingila da ke aiki a matsayin masu tallafawa bakin haure kuwa, za a…
Read More