Editor

9513 Posts
Firaministan Haiti ya kama hanyar murabus saboda matsin lambar ‘yan daba

Firaministan Haiti ya kama hanyar murabus saboda matsin lambar ‘yan daba

Firaministan Haiti Ariel Henry ya yada ƙwallon mangoro domin hutawa da ƙuda, wajen miƙa murabus ɗinsa a matsayin shugaban ƙasar da ke yankin Caribbean, bayan cimma matsaya da ƙungiyar ƙasashen yankin a matsayin mafita na warware rikicin siysar ƙasar. Shugaban ƙungiyar ƙasashen yankin Caribbean kuma shugaban ƙasar Guyana Irfaan Ali, wanda ya tabbatar da shirin murabus din Henry, ya yaba da matakin da ya kira wata dama ta kafa kwamitin shugaban ƙasa na riqon ƙwarya wanda zai naɗa firaministan riƙon kwarya. Henry mai shekaru 74 wanda ke riƙe da kujerar firanministan Haiti da ba zaɓen sa aka yi ba tun…
Read More
Atiku, Yari da Ningi suna yunƙurin kafa sabuwar jam’iyyar siyasa

Atiku, Yari da Ningi suna yunƙurin kafa sabuwar jam’iyyar siyasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A cikin makon nan ne dai jaridar The Nation ta samu labarin cewa 'yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar da za ta tunkari jam’iyyar APC mai mulki a babban zaɓe mai zuwa. Gabanin shekarar 2027, majiyoyi sun ce ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zacen shekarar da ta gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya ƙaddamar da ƙudirin jam’iyyar da ake son a yi tare da haɗin gwiwar wasu 'yan majalisar dokokin ƙasar. An tattaro cewa, sansanin Atiku na taka-tsan-tsan da rashin haɗin kan da ke cikin babbar jam’iyyar adawa, yana tunanin cewa idan ta…
Read More
Yadda Tinubu ya dakatar da shirin bada lamuni ga ɗalibai

Yadda Tinubu ya dakatar da shirin bada lamuni ga ɗalibai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An ɗage ƙaddamar da shirin bayar da lamuni ga ɗaliban Nijeriya wanda aka shirya fara shi a gwamnatin Bola Tinubu, sa'o'i 48 gabanin ƙaddamarwa. Akintunde Sawyer, Babban Sakataren Hukumar Kula da Lamuni ta Ilimi ta Nijeriya (NELFUND) ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da ya yi da gidan talabijin na AriseTV a ranar Talata. Tun da farko an shirya farawa shirin ne a ranar Alhamis, amma an sake jingine ƙaddamar da shi, yayin da ake yin gyare-gyare don tabbatar da shirin cikin inganci ba tare da wata matsala ba, a cewar Sawyer.  "Ba zan iya…
Read More
Ɗaliban Kuriga: Tinubu ya ƙi amincewa da tayin Sheikh Gumi na tattaunawa

Ɗaliban Kuriga: Tinubu ya ƙi amincewa da tayin Sheikh Gumi na tattaunawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya ƙi amincewa da tayin Sheikh Gumi na tattaunawa da ‘yan bindiga kamar yadda ya umurci hukumomin tsaro a ƙasar nan da su tabbatar an dawo da duk waɗanda aka yi garkuwa da su a sassa daban-daban na ƙasar nan. Idan dai za a iya tunawa, an samu ƙaruwar satar mutane musamman a yankin Arewa maso Yamma na qasar nan a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata, inda lamarin neman kuɗin fansa ke ƙaruwa. Wasu gungun masu garkuwa da mutane da suka yi garkuwa da mutane 16 a yankin Gonin-Gora da…
Read More
’Yar’Adua ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa

’Yar’Adua ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sanata mai wakiltar Katsina ta Tsakiya a Majalisar Dokokin Nijeriya, Abdulaziz Musa Yar’Adua, ya zama sabon Shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa. An naɗa ’Yar’Adua, ɗan majalisa na jam’iyyar APC, a matsayin sabon shugaban ƙungiyar kwanaki biyu bayan dakatar da Sanata Abdul Ningi. Ningi, mai wakiltar Bauchi ta tsakiya, ya zargi babban zauren majalisar da karkatar da kasafin kuɗin shekarar 2024 har na naira tiriliyan 3.7. Duk da cewa batun ƙara kasafin kuɗi ba sabon abu ba ne a Nijeriya, amma wannan ne karon farko da wani ɗan majalisar dattawa da ya taka rawar gani wajen zartar da…
Read More
An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kamaru ta dakatar da 'yan wasan ƙasar 62 bisa laifin coge wajen bayyana shekaru, cikinsu har da matashi mafi ƙarancin shekaru a tawagar da ta buga gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a watan Janairu. Hukumar ta FECAFOOT ta fitar da jerin sunayen a hukumance a ƙarshen wannan makon, ciki harda Wilfried Nathan Douala mai shekaru 17 wanda ya ba da mamaki cikin tawagar Rigobert Song a gasar da aka kammala a Ivory Coast. A cewar FECAFOOT, mai tsaron ragar Victoria United ya yi ƙarya game da shekarunsa, don haka an hana…
Read More
An karrama marubuci Abba Abubakar Yakubu

An karrama marubuci Abba Abubakar Yakubu

Daga HABU ƊAN SARKI a Jos Fitaccen marubucin nan kuma jarumin finafinan Kannywood, Ado Ahmad Gidan Dabino (MON) ya taɓa faɗa cewa, 'Duk wani abu mai kyau da ka ke yi duniya tana gani, kuma wata rana za ka samu sakamakonsa.' Wannan bayani nasa ne ya fito a fili jama'a suka shaida, a ƙarshen makon da ya gabata, inda wata cibiya mai koyar da ilimin fasahar sadarwa da kula da adana littattafai, wato Information and Library Science, mai suna Majema College of Advanced Studies Jos ta karrama marubuci kuma ɗan jarida, Abba Abubakar Yakubu, sakamakon jajircewa da gudunmawar da yake…
Read More
Gwamna Lawal ya biya ma’aikatan Zamfara kuɗin hutu

Gwamna Lawal ya biya ma’aikatan Zamfara kuɗin hutu

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Dauda Lawal na jihar Zamfara ya amince kan a biya ma'aikatan jihar kuɗin hutu domin ba su damar yin walwala a cikin watan Ramadan. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce tuni ma'aikatan jihar suka fara samun biya a Larabar wannan makon. Sanarwar manema labarai da Sulaiman ya fitar ta ce, kuɗin hutun kashi 10 cikin 100 ne na albashin da ma'aikaci ke ɗauka a shekara. Sanarwar ta ƙara da cewa, tun bayan da Lawal ya karɓi ragamar mulkin jihar, gwamnatinsa ta ɗauki lamarin walwalar ma'aikatan jihar da wasa ba. Don kuwa, “Ya…
Read More
Yadda marubutan adabi suka yi bikin Ranar Marubuta ta 2024

Yadda marubutan adabi suka yi bikin Ranar Marubuta ta 2024

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ana gudanar da bikin Ranar Marubuta ta Duniya ne a ranar 3 ga watan Maris na kowacce shekara, domin ƙara zaburar da marubuta a ko'ina a duniya game da gudunmawar da suke bayarwa wajen faɗakarwa da ilimantar da jama'a da suke yi, musamman matasa da ɗaliban ilimi. Tun a shekarar 1986 aka fara bikin ranar a faɗin duniya, bayan shawarwarin da ƙungiyoyin marubuta da mawaqƙa daban-daban suka riƙa bayarwa don ganin an ware wata rana guda da za a riƙa tattauna abubuwan da suka shafi harkar rubutu da basirar ƙirƙira. Sau da dama jama'a sun fi…
Read More
Tsaro: Lawal ya rattaɓa hannu kan wasu sabbin dokoki

Tsaro: Lawal ya rattaɓa hannu kan wasu sabbin dokoki

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya rattaba hannu kan wasu sabbin dokoki da suka haɗa da doka haramta amfani da gilashin mota mai duhu da sayar da burodi mara ɗauke da shaida. Sauran hanin sun haɗa da ɗura burodi a buhu da kuma saida fetur sama da lita 50 a lokaci guda ga abubuwan hawa. A ranar Talata Gwamna Lawal ya sanya wa dokokon hannu don su fara aiki a jihar. Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce doka mai lamba 02 da mai lamba 04, 2024, za su taimaka wajen daƙile abubuwan da suke haifar…
Read More