Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kamaru ta dakatar da ‘yan wasan ƙasar 62 bisa laifin coge wajen bayyana shekaru, cikinsu har da matashi mafi ƙarancin shekaru a tawagar da ta buga gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a watan Janairu.
Hukumar ta FECAFOOT ta fitar da jerin sunayen a hukumance a ƙarshen wannan makon, ciki harda Wilfried Nathan Douala mai shekaru 17 wanda ya ba da mamaki cikin tawagar Rigobert Song a gasar da aka kammala a Ivory Coast.
A cewar FECAFOOT, mai tsaron ragar Victoria United ya yi ƙarya game da shekarunsa, don haka an hana ɗan wasan shiga wasannin share fage na Elite League.
Ba a bayyana ainihin shekarun Douala ba, amma lamarin haɗa da wasu ‘yan wasa 61 da aka dakatar saboda ƙin bayyana shekarun su na asali.
Matakin na zuwa ne a daidai lokacin hukumar FECAFOOT ƙarƙashin jagorancin Samuel Eto’o ke da nufin rage matsalolin gudanarwa da aka fuskanta a baya a lokacin da kuma bayan kammala kakar wasan ƙwallon ƙafa ta Kamaru.