16
Feb
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta janye tuhumar da ta ke yi wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar AAC kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyole Sowore. Gwamnatin Tarayyar ta janye tuhumar ce da ta ke yi na zargin cin amanar ƙasa a kansa a ranar Laraba 14 ga watan Faburairu. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Babbar Kotun Tarayya ta fitar a ranar Laraba 14 ga watan Faburairu. Antoni Janar na Gwamnatin Tarayya, Lateef Fagbemi shi ya miƙa takardar dakatar da tuhumar kan mamallakin gidan jaridar Sahara Reporters. Sanarwar ta ce, "Duba da sashi na…
