Editor

9513 Posts
Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Daga BASHIR ISAH Shugabannin ƙasashen Afirka ƙarƙashin Ƙungiyar Haɗi Kan Afirka (AU) sun zaɓi Shugaban Ƙasar Mauritania, Mohamed Ould Ghazouani, a matsayin sabon shugaban AU na 2024. Ghazouani ya gaji wannan kujera ne daga Shugaba Azali Assoumani na ƙasar Comoros, wanda ya yi riƙe shugabancin ƙungiyar a 2023. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya Bankin Access ya naɗa sabuwar Babbar jamiar zartarwar rukunin bankunan ta riƙon ƙwarya An yi zaɓen a ranar Asabar, 17 ga Fabrairu yayin babban taron ƙungiyar karo na 37 wanda ke gudana a Addis Ababa, babban birnin Habasha.
Read More
Gwamnatin Tinubu ta tsayar da ranar ganawa da su Ɗangote kan tsadar siminti

Gwamnatin Tinubu ta tsayar da ranar ganawa da su Ɗangote kan tsadar siminti

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu, ta kira taron gaggawa tare da kamfanoni masu samar da siminti domin tattauna tashin farashin siminti a ƙasa. Kafar Nairametrics ta rawaito cewa, a halin yanzu farashin buhun siminti mai nauyin 50kg a sassan Legas ya kai N9,500. Majiyar ta ƙara da cewa a watan Janairun da ya gabata, farashin buhun simintin bai wuce N6,000 zuwa N6,500 a nan Legas ɗin ba. Tuni dai wasu ƙananan ‘yan kasuwa suka daina sayar da siminti don gudun abin da ka je ya dawo na hauhawar farashinsa. Sai dai a matsayin wani mataki…
Read More
Bankin Access ya naɗa sabuwar Babbar jamiar zartarwar rukunin bankunan ta riƙon ƙwarya

Bankin Access ya naɗa sabuwar Babbar jamiar zartarwar rukunin bankunan ta riƙon ƙwarya

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Bankin Access ya ba da sanarwar naɗin Mis Bolaji Agbede a maysayin Babbar Jami'ar Zartarwar Bankin ta riƙon ƙwarya. Wannan naɗin ya biyo bayan rasuwar tsohon Babban Jami'in Zartarwar bankin mai suna Dakta Herbert Wigwe. A ranar 9 ga watan Fabrairu, 2024. Mista Wigwe ya rasu a haɗarin jirgi mai saukar ungulu tare da matarsa da ɗansa da kuma tsohuwar shugabar Kamfanin canji na Nijeriya, Abimboloa Ogunbanjo a ranar Juma'a. A wani jawabi na shugaban kwamitin daraktocin bankin ya yi ranar 12 ga Fabrairu, 2024 ya bayyana…
Read More
’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya

’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ’Yan Majalisar Wakilai sama da 60 ne ke neman a yi wa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya kwaskwarima zuwa tsarin da ke ɗauke da Fira Minista kamar yadda aka faro a ƙasar.  A ƙarƙashin jagorancin Wale Raji, ɗan majalisar wakilai na jam’iyyar APC mai wakiltar Jihar Legas, sun nemi sauyi a Kundin Tsarin Mulkin ƙasar. Daga cikin hujjojinsu akwai rage yawan kashe kuɗaɗe wurin gudanar da mulki da samar da tsare-tsare. Har ila yau, masu goyon bayan ƙudurin sun tabbatar da cewa sabon tsarin ba zai fara aiki yanzu ba, zai iya kai wa zaɓen shekarar 2031.…
Read More
Tsohon soja mai kai wa ’yan ta’adda kayan sojoji ya shiga hannu

Tsohon soja mai kai wa ’yan ta’adda kayan sojoji ya shiga hannu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar 'Yan Sandan Nijeriya ta kama wani tsohon jami’in sojan saman Nijeriya, bisa samunsa da hannu wajen samar da kakin soja ga ’yan bindiga da suka addabi Jihar Zamfara. An bayyana sunan sa da Ahmed Mohammed, jami’in da aka kora, wanda a baya yana aiki a sansanin sojin sama da ke Kaduna, ya aikata wannan ta’asa ne bayan kotu ta gurfanar da shi bayan wani laifin da sojoji suka aikata da ba a bayyana ba. Kakakin rundunar ’yan sandan ACP Muyiwa Adejobi ya bayyana cewa Mohammed ya haɗa kai da Mushiri Abubakar wajen raba kayan sojoji…
Read More
Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Rahana Ibrahim Bunzawa wacce ta lashe gasar iyo (Linƙaya) wato tsere cikin ruwa ta ce ta yi bankwana da wannan wasa na ruwa har abada. Ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke ganawa da wakilinmu a garin Yawuri jim kaɗan bayan kammala bikin 'Rigata' da aka gudanar kwanan nan. Ta ce wannan shi ne karo na biyu da ta ke lashe wannan gasar a jere kuma a duk lokacin da ta shiga ita ce samun nasara saboda haka ta yi bankwana da shiga gasar Rigata daga bana. "Na soma shiga gasar tun…
Read More
Akwai hanyoyin magance matsalar tsaro da yunwa, aiwatarwa ne matsala – Sarkin Musulmi 

Akwai hanyoyin magance matsalar tsaro da yunwa, aiwatarwa ne matsala – Sarkin Musulmi 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ce jagororin Arewan Nijeriya sun san hanyoyin da za a magance matsalar tsaro da talauci da yunwa da suka addabi yankin, amma ba su yi a aikace. Sarkin Musulmi ya shaida wa taron sarakuna da jagororin Arewa cewa yadda matsalar rashin tsaro da rashin aikin yi da kuma talauci, musamman a tsakanin matasan Arewacin Nijeriya, babbar barazana ce ga ƙasar. Da yake jawabin da taron da suka gudanar a Kaduna, Sarkin Musulmi, ya bayyana cewa yanzu ’yan Nijeriya a fusace suke, saboda yunwa da talauci, ga kuma “durƙushewar…
Read More
Tsadar Rayuwa: NLC za ta gudanar da zanga-zangar gama-gari na yini biyu

Tsadar Rayuwa: NLC za ta gudanar da zanga-zangar gama-gari na yini biyu

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta sanar da shirya zanga-zangar gama-gari na yini biyu domin nuna rashin jin daɗinta dangane da tsadar rayuwar da ake fuskanta a Nijeriya. Ƙungiyar ta ce za ta gudanar da zanga-zangar ne a ranakun 27 da 28 ga Fabrairun 2024. Shugaban NLC na ƙasa, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan yayin taron gaggawar da ƙungiyar ta shirya ranar Juma'a a babban ofishinta da ke Abuja. Joe ya ce, “Abin da takaici tura mu da aka yi zuwa ga ɗaukar wannan mataki, sai dai ci gaba da yin biris da ake yi game…
Read More
Yadda bikin ‘yar marubuciya Bilkisu Ali ya ƙayatar

Yadda bikin ‘yar marubuciya Bilkisu Ali ya ƙayatar

DAGA MUKHTAR YAKUBU An daura auren Sarra Tasi'u Ya'u Babura 'yar marubuciya 'yar Jarida kuma malama a Jami'ar Alqalam Hajiya Bilkisu Yusuf Ali tare da yin tarukan biki na kece raini. An daura auren Sarra Tasi'u Babura da angota Salihu Ibrahim Darma (Khalifa) ne dai a ranar Juma'a 9 ga Fabarairu 2024 ne a gidan Imam Sheikh Dr. Yusuf Ali da ke Unguwar Tudun Maliki ta Karamar Hukumar Kumbotso a cikin garin Kano da misalin 2-30 na rana inda dumbin jama'a suka halarci daurin auren. Bayan daurin auren ne kuma uwar amarya ta shirya taron wuni a wajen taro na…
Read More
CBN ya dakatar da kamfanonin mai biyan kashi 100 a ƙasar waje

CBN ya dakatar da kamfanonin mai biyan kashi 100 a ƙasar waje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya dakatar da kamfanonin mai na ƙasa da kasa mayar da kashi 100 na kuɗaɗen musaya na ƙasashen waje zuwa ga kamfanonin ƙasashen waje a lokaci guda. Bankin ya ce, kamfanonin mai na ƙasa da ƙasa na iya mayar da kashi 50 na kuɗaɗen da suka samu a matakin farko sannan sauran rabin bayan kwanaki 90. Daraktan sashen ciniki da musayar kuɗi na babban bankin, Hassan Mahmud ne ya bayyana haka a wata takardar da aka fitar mai ɗauke da kwanan wata 14 ga Fabrairu, 2024. Babban bankin na CBN…
Read More