Editor

9513 Posts
EFCC na neman matar Emefiele ruwa a jallo bisa zargin almundahana

EFCC na neman matar Emefiele ruwa a jallo bisa zargin almundahana

Daga BASHIR ISAH Hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC ta ce tana neman matar tsohon Gwamnan CBN, Margaret Emefiele da wasu mutum uku ruwa a jallo a kan batun da ya shafi almundahana. Majiyarmu ta bayyana cewa a daren Juma'ar da ta gabata EFCC ta sanar da neman da take yi wa Mrs Emefiele da Mr Eric Odoh da Anita Omoile tare da mijinta Jonathan Omoile. Hukumar na neman waɗanda lamarin ya shafa ne bisa zargin haɗin baki da tsohon Gwamnan na CBN "wajen karkatar da maƙudan kuɗi mallakar Gwamnatin Tarayya wanda hakan ya sa suka mallaki kuɗi ta hanyar…
Read More
’Yan sanda sun kama masu garkuwa da mutane a Abuja

’Yan sanda sun kama masu garkuwa da mutane a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar 'yan sandan Nijeriya a Abuja, babban birnin ƙasar ta ce ta kama wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutanen ne domin neman kuɗin fansa a wani yanki na birnin. A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun mai taimaka mata kan hulɗa da jama'a, Josephine Adeh, rundunar ta ce ta samu nasarar hakan ne a wani samame da ta kai a wani Otal da ke ƙauyen Bassa, bayan samun wasu bayanan sirri. Abuja, babban birnin Nijeriya na fuskantar matsalar tsaro a cikin watanni na baya-bayan nan. Matsalar garkuwa da…
Read More
Matasa a Kano sun gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa

Matasa a Kano sun gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Matasa maza da mata da dama a jihar Kano sun fito domin gudanar da zanga-zanga don nuna adawarsu da tsadar kayan masarufi da ake fuskanta a Nijeriya. Masu zanga-zangar dai sun fito ɗauke da kwalaye, inda suke rera waƙa mai taken “Tsadar rayuwa ba za mu iya ba”, a ƙoƙarin da suke yi na nuna halin da suke ciki. Matasan waɗanda suka fito fuskokinsu a murtuke, sun gudanar da zanga-zangar ne a ranar Alhamis a unguwannin Bachirwa, Kurna da kuma Rijiyar lemo, da ke kan titin zuwa Katsina a Kano. Kazalika, masu zanga-zangar dai sun…
Read More
PDP ta ƙara ba Shugaban Matasan jam’iyyar na ƙasa dama a karo na biyu – Mannir Abdullahi

PDP ta ƙara ba Shugaban Matasan jam’iyyar na ƙasa dama a karo na biyu – Mannir Abdullahi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An yi kira ga uwar Jam'iyyar PDP ta ƙasa, da ta ƙara bai wa Shugaban Matasan Jam'iyyar na Ƙasa dama a karo na biyu domin ƙara ƙarfafa wa matasa a sha'anin shugabanci. Kakakin gamayyar ƙungiyoyin matasa na Arewacin Nijeriya, Kwamared Mannir Abdullahi Giwa shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai jiya Alhamis. Kwamared Mannir ya ce tunda aka ba Nijeriya 'yancin kai a 1960 aka kuma fara mulkin dimukraɗiyya ba a tava shugaban matasa na kasa mai ƙoƙari da sanin makamar aiki kamar Prince Muhd Kadaɗe Suleiman ba,…
Read More
HOTUNA: An ɗaura auren ‘yar Dokta Bilkisu Ali

HOTUNA: An ɗaura auren ‘yar Dokta Bilkisu Ali

A ranar Juma'a, ga ga Fabrairu aka ɗaura auren 'yar Dokta Bilkisu Yusuf Ali, Sarrah Tasiu Yau da angonta Salhu Ibrahim Darma (Khalifa) a Kano. An ɗaura auren ne a masallacin marigayi Imam Sheikh Dr. Yusuf Ali da ke cikin garin Kano bayan da aka sauko daga Sallar Juma'a. Dokta Bilkisu shahararriyar marubuciya ce kuma malamar jami’a, kuma 'ya ga Marigayi Imam Yusufa Ali. Babban Editan jaridar Blueprint Manhaja, Nasiru S. Gwangwazo na daga cikin waɗanda suka shaida ɗaurin auren. Sauran mahalartar sun haɗa da marubuta kamar Farfesa Yusuf Adamu, Bala Anas Babinlata, Larabi, Adamu Yusuf Indabo, Zahraddin Kallah, Lubabatu…
Read More
Ya dace a farfaɗo da gidajen ilimi a Zariya – Farfesa Maƙari

Ya dace a farfaɗo da gidajen ilimi a Zariya – Farfesa Maƙari

Daga ISAH GIDAN ƁAKKO a Zariya Babban limamin masallacin Abuja Farfesa Ibrahim Maqari Sa'id ya shawarci masarautar Zazzau ta ɗora ɗambar farfaɗo da gidajen ilimi da suka yi silar Zariya ta zama birnin ilimi fiye da shekara ɗari da suka gabata. Farfesa Maqari ya bayar da wannan shawarar ce a lokacin taron Mauludin da ya saba jagoranta a ƙarƙashin shugabancinsa da taron ya gudana a fadar Zazzau. Ya bayar da misalan wasu gidaje a birnin da ya ce a ciki da wajen Nijeriya a na zuwa Zariya domin neman ilimin addini na fannoni daban-daban da ɗan lokaci, sai wanda ya…
Read More
An bankaɗo yadda Kotun Ƙoli ta yi sama-da-faɗi da Naira biliyan 12 lokacin mulkin Buhari

An bankaɗo yadda Kotun Ƙoli ta yi sama-da-faɗi da Naira biliyan 12 lokacin mulkin Buhari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rahoton bin diddigin ayyuka da aika-aikar da aka tafka a Kotun Ƙoli, wanda Ofishin Akanta Janar na Ƙasa ya fitar, ya bayyana cewa an yi ba daidai ba wajen kashe Naira biliyan 12, tsawon shekaru biyar a kotun. Ofishin Akanta Janar ya ce Kotun Ƙoli ba ta kashe kuɗaɗen ba bisa ƙa’ida ba, don haka a gaggauta maida su asusun gwamnatin tarayya. Rahoton ya umarci Babban Rajistara na Kotun Ƙoli cewa ya maida kuɗaɗen aljihun gwamnati da gaggawa. An dai fitar da rahoton tun cikin watan Disamba, kuma ya faɗo hannun Blueprint Manhaja, ta…
Read More
Shugaban UBEC ya buƙaci a riƙa koyarwa da harshen uwa a makarantu

Shugaban UBEC ya buƙaci a riƙa koyarwa da harshen uwa a makarantu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja UBEC ta gano rashin halin ko-in-kula da ake saka wa wajen aiwatar da manufofin harshe kan amfani da harshen uwa a makarantu a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaban muradun ƙarni masu ɗorewa, SDGs, a Nijeriya. Sakataren zartarwa na hukumar kula da ilimin bai ɗaya ta ƙasa ,UBEC, Dr Hamid Bobboyi ne ya bayyana haka a wani taron masu ruwa da tsaki a Abuja a ranar Litinin. Taron na masu ruwa da tsaki na kwanaki biyu mai taken “Tattaunawa kan samar da dabaru na Karatu a Cikin Shirin…
Read More
Kamaru ta ƙi amincewa da murabus ɗin Eto’o

Kamaru ta ƙi amincewa da murabus ɗin Eto’o

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ƙasar Kamaru, ta ƙi amincewa da buƙatar ajiye aiki da tsohon ɗan wasan gaba na ƙasar, Samuel Eto’o, ya gabatar mata. A ranar Litinin ne, Eto’o ya miƙa takardar ajiye muƙamin shugabancin hukumar, yayin wani taron ganawa da aka gudanar a birnin Yaounde. Tsohon ɗan wasan na Kamaru ya ce matakin nasa ya biyo bayan gazawar ’yan wasan ƙasar na ƙasa taɓukawa a gasar kofin nahiyar Afirka ta AFCON da ke gudana a ƙasar Ivory Coast. Sai dai mambobin hukumar sun ce suna da qƙwarin gwiwa a kansa na ci gaba da aiwatar…
Read More
Makarantar Ihya’us-sunnah ta yaye ɗalibai bakwai karo na farko a Legas

Makarantar Ihya’us-sunnah ta yaye ɗalibai bakwai karo na farko a Legas

Daga DAUDA USMAN a Legas Makarantar Ihya'us-sunnah Islamiyya a unguwar Mile-12 Intanashinal Market dake cikin birnin Legas a ƙarƙashin jagorancin shugaban kwamitin makarantar Alhaji Salisu Madobi Mai Barkono ta gudanar da taron walimar yaye ɗalibai maza da mata bakwai karo na ɗaya a Legas tare da neman taimakon zunzurutun kuɗi har Naira miliyan ashirin domin kammala ginin makarantar tare da faɗaɗa a zuzuwanta da sauran harkokin ayyukanta bakiɗaya. Taron walimar yaye ɗaliban wanda ya gudana a makarantar Maidan Primary School dake unguwar Mile-12 ranar Lahadin makon jiya, manyan baqin malamai a wajen taron walimar sun haɗa da shugaban ƙungiyar Izala…
Read More