09
Feb
Daga ISAH GIDAN ƁAKKO a Zariya A ranar Juma'ar da ta gabata Mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya jagoranci buɗe masallacin juma'a a garin Fammadina a gundumar Dutsen Abba da ke Zariya. Taron buɗe masallacin ya samu halartar wanda ya gina masallaci wato Alhaji Umar Faruq Suleiman da masana ilimin addinin Musulunci da kuma fitattun 'yan siyasa da suke ciki da wajen jihar Kaduna. Mai martaba Sarkin Zazzau a jawabinsa ya fara da addu'a ta musamman ga wanda ya gina masallacin a cikin lokaci ba mai tsawo ba. Malam Ahmed Bamalli ya kuna matuƙar jin daɗinsa na…
