Editor

9513 Posts
Kotu ta bai wa gwamnatin Tinubu umarnin daidaita farashin kayayyaki cikin mako guda

Kotu ta bai wa gwamnatin Tinubu umarnin daidaita farashin kayayyaki cikin mako guda

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Ikoyi, Jihar Legas ce ta ba da wannan umarni a ranar Laraba, 7 ga Fabrairu. Umarnin Kotun ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta daidaita farashin fetur da na saura kayayyaki a cikin mako daya. Mai Shari’a Ambose Lewis-Allagoa ne ya ba da wannan umarni biyo bayan karar da Babban Lauyan Nijeriya kuam mai rajin kare hakkin dan’adam, Femi Falana SAN ya shigar Kotun. A cewar Alkalin, “Na ji mai karar Femi Falana a cikin kararsa mai lamba FHC/L/CS/869/2023 kuma na gano duk da karar da aka shigar kan masu kare kansu,…
Read More
‘Yan bindigar da suka sace ‘yan rakiyar amarya 63 a Katsina sun saki bidiyo

‘Yan bindigar da suka sace ‘yan rakiyar amarya 63 a Katsina sun saki bidiyo

Daga UMAR GARBA a Katsina 'Yan bindigar da suka sace mutane 63 dake kan hanyarsu ta kai amarya gidan mijinta sun saki bidiyo inda suka nuna fuskokin wadanda ake garkuwar da su. Abubuwan da bidiyon ya kunsa shi ne, 'yan bindigar sun fara kalubalantar jami'an tsaro inda suka bayyana cewa idan akwai wanda zai iya karbar mutanen ya zo ya jaraba, ya ga abun da zai faru da shi. Sun kuma bayyana cewar idan ba a fanshi amaryar ba kan lokaci za su sake aurar da ita ga wani mijin. A cikin bidiyoyin wadda yanzu haka ta karade safukan sada…
Read More
Manomi ya yi wa Gwamna Bago kyautar doya don yaba ƙoƙarinsa

Manomi ya yi wa Gwamna Bago kyautar doya don yaba ƙoƙarinsa

Daga BASHIR ISAH Wani manomi a Jihar Neja ya yi wa Gwamnan Jihar, Umaru Mohammed Bago, kyautar luka-lukan doya domin yaba masa da kuma nuna farin cikinsa game da aikin cigaban al’umma da ke gudana a jihar.   Da yake zantawa da shafin Tsalle Daya, Abdullahi Umar ya ce bayan da ya shigo garin Minna, babban birnin jihar ya ga irin ayyukan da Bago ke yi, hakan ya sa ya ga dacewar shirya masa wannan kyauta domin yaba kokarinsa. Mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin siyasa da tsare-tsare, Nma Kolo ne ya karbi doyar a madadin Gwamnan, inda ya…
Read More
NAPPS ta buƙaci Gwamnatin Katsina ta sassauta haraji

NAPPS ta buƙaci Gwamnatin Katsina ta sassauta haraji

Daga WAKILINMU Kungiyar Masu Makarantu Masu Zaman Kansu, watau National Association of Proprietors of Private Schools (NAPPS) reshen jihar Katsina ta roki Gwamnatin jihar Katsina ta rage yawan harajin da hukumomi ke amsa wurin makarantu masu zaman kansu. Shugaban kungiyar Alhaji Mansur Sani Jibia ne ya yi wannan kiran a yayin wani taro da kungiyar ta shirya kuma ta gayyaci masu ruwa da tsaki. Katsina Post ta ruwaito cewa, hukumomin da kungiyar ta gayyata sun hada da hukumar tara kudaden shiga (IRS), sai kuma ma'aikatar ciniki da masana'antu. Shugaban kungiyar ya koka akan yadda membobin kungiyar ke fuskantar matsi lamba…
Read More
Ta haifi ’yan huɗu yayin yi wa ƙasa hidima

Ta haifi ’yan huɗu yayin yi wa ƙasa hidima

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata ’yar Nijeriya, wadda a halin yanzu take tsaka da yi wa kasa hidima (NYSC) ta haifi ’ya’ya hudu a yayin yi wa kasa hidima. Wani faifan bidiyo da ke zagayawa a yanar gizo an yi masa taken, “Haihuwar 'ya’ya hudu yayin hidima” kuma ya nuna matashiyar sanye da kakin NYSC. A cikin faifan bidiyon, mahaifiyar da ke tsaye kusa da wani mutum-mutumi a sakatariyar NYSC, cikinta ya bayyana da girma. A cikin shirin na biye, matar ta matsa kusa da kyamarar, ta bayyana fuskarta. Bidiyon ya nuna fuskokin jarirai hudu da ta haifa. Masu amfani…
Read More
Ƙungiyar NANAS ta aurar da mutane 300 a Kebbi

Ƙungiyar NANAS ta aurar da mutane 300 a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi A karon farko da aka gudanar da auren mutane dari uku a fadar Mai Girma Sarkin Gwandu Alhaji Muhammadu Iliyasu Bashar a karkashin wata kungiya mai suna NANAS da matar gwamnan jihar Kebbi Hajiya Nafisa Nasiru Idris ke jagoranta. Shi dai wannan auren sabanin irin aure-aure ne da aka saba shiryawa ba kamar na marayu ko zawarawa ba, wannan auren aure ne na marasa galihu irin wadanda ake saka rana ana dagawa saboda rashin abin auren ko kuma rashin abinda za a yi wa amarya kayan daki daga bangaren iyayen mace wanda ya kunshi…
Read More
Binciken tsaro ya bankaɗo shirin neman gwara kan Sanatocin Arewa da na ’yan ƙasa

Binciken tsaro ya bankaɗo shirin neman gwara kan Sanatocin Arewa da na ’yan ƙasa

Daga BASHIR ISAH Wasu jami’an hukumomin tattara bayana asirri na kasa sun bankado shirin da wasu makirai ke yi na neman gwara kan sanatocin Arewa a Majalisar Tarayya  da talakawansu. Jami’an wadanda suka bukaci a sakaya sunansu su shaida wa jaridar PRNigeria cewa har wa yau, shirin na da nufin gwara kan hukumomin tsaron kasar nan don su rika ganin laifin juna game da matsalar tsaron kasa. Sun bayyana hakan ne a matsayin martani a kan wani rahoto wanda ya yi zargin hukumomin tsaron sun kafa idanunsu kan wani Sanatan Arewa saboda zarginsa da ake yi da daukar nauyin ta’addanci,…
Read More
Yadda garkuwa da ‘yan mata ya zama kasuwanci

Yadda garkuwa da ‘yan mata ya zama kasuwanci

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Batun satar mutane ana garkuwa da su don neman kuɗin fansa ba sabon abu ba ne, musamman ga yara mata, ko ɗaliban makarantu da sauransu. Sai dai wani sabon salo da gungun waɗannan ɓatagari suka ɓullo da shi shi ne satar 'yan mata a cikin birnin Abuja. Na san kuna da labarin 'yan matan nan su biyar da aka yi garkuwa da su, har ma aka kashe wata daga ciki, mai suna Nabeeha. Waɗanda ba a jima da karɓo fansar su ba. Sai kuma ga shi da safiyar ranar Laraba da ta gabata an samu…
Read More
Tinubu ya isa Abuja bayan kammala ziyara a Faransa

Tinubu ya isa Abuja bayan kammala ziyara a Faransa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Bola Tinubu ya isa birnin tarayya, Abuja, bayan kammala ziyara a kasar Faransa domin gudanar da harkokinsa. Tinubu ya sauka filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da misalin karfe 8:50 na dare inda ya samu tarba daga tawagar gwamnati karkashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume. Haka nan, tawagar takunshi manyan jami'ai irin su Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila; Ministan Abuja, Nyesom Wike da sauransu. Tun a ranar Laraba ta makon jiya Tinubu ya bar Nijeriya zuwa Faransa, kuma wannan ita ce ziyararsa ta biyu a kasar tun…
Read More
Ƙasurgumin ɗan fashin dajin da ya addabi Birnin Gwari ya shiga hannu a hanyarsa ta zuwa kafa sansani a Kano

Ƙasurgumin ɗan fashin dajin da ya addabi Birnin Gwari ya shiga hannu a hanyarsa ta zuwa kafa sansani a Kano

Daga BASHIR ISAH Jami’an tsaro a Kano sun cika hannu da gawurtaccen dan fashin dajin nan da ya addabi yankin Birnin Gwari, Isah Lawal. Dan bindigar ya fada a komar ‘yan sandan ne bayan da ya shirya zuwa kafa sansani a Kano inda aka same shi dauke da shanu 55 da tumaki guda shida, kamar yadda Kakakin ‘Yan sandan Kano, ASP Abdullahi Haruna ya bayyana a ranar Litinin. ‘Yan sanda sun ce wanda ake zargin a baya mazaunin kauyen Kaya ne da ke yankin Karamar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna. Jami’an sun ce dan fashin dajin ya yi ikirarin cewa…
Read More