Editor

9513 Posts
Mutum 2 sun mutu a harin da aka kai gidan Gwamna Uzodinma a Imo

Mutum 2 sun mutu a harin da aka kai gidan Gwamna Uzodinma a Imo

Daga WAKILINMU Sahihan bayanai daga jihar Imo sun tabbatar da wasu mutum biyu sun rasa rayukansu yayin harin da 'yan bindiga suka kai wa gidan Gwamna Uzodinma da ke Omuma a yankin karamar hukumar Oru ta Yamma a jihar. Wannan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da gwamnan ya sanar da manema labarai cewa an yi nasarar kama wasu mutum 50 da ake zargi suna da hannu a hare-haren da aka kai a Imo lokacin bikin Easter da ya gabata, tare da cewa wasu 'yan siyasa ne suka ɗauki nauyinsu. Sai dai Manhaja ba ta samu tabbacin faruwar hakan ba…
Read More
Mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam ta rasu

Mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam ta rasu

Daga UMAR M. GOMBE Allah Ya yi wa mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam Ado Bayero rasuwa. Bayanai daga masarautar Kano sun nuna marigayiyar ta rasu ne a wannan Lahadi a wata asibitin birnin Alƙahira a Kasar Misra, bayan fama da ta yi da rashin lafiya. Hajiya Maryam ta rasu tana da shekara 86 a duniya. Kuma ita ce mahaifiyar Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado Bayero. Ya zuwa haɗa wannan labari, Masarautar Kano ba ta kai ga bada sanarwar lokacin da za a gudanar da jana'izar marigayiyar ba. Manhaja ta kalato cewa marigayiyar tsohuwar…
Read More
An bai wa kasuwar fanteka ta Kaduna wa’adin mako guda ta tashi

An bai wa kasuwar fanteka ta Kaduna wa’adin mako guda ta tashi

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Raya Birane ta Jihar Kaduna, ta bai wa 'yan kasuwar sabuwar Kasuwar Fanteka wa'adin mako guda a kan su tattara yanasu-yanasu su bar kasuwar. Cikin wata sanarwar mai ɗauke da kwanan wata 22, Afrilu, 2021wadda ta sami sa hannun Babban Daraktan Hukumar, Isma'ila Ummaru Dikko, hukumar ta ce wannan umarni ya soma aiki ne daga ranar da aka bada shi. Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne daidai da Shirin Sabunta Biranen Jihar na Gwamnatin Jihar. Da wannan gwamnatin jihar ta ce ta bai wa 'yan kasuwar wa'adin kawana bakwai a kan kowa ya kwashe…
Read More
Ƙagaggen rubutu tamkar ɗa ne wajen mahaifinsa Adabi, shi ko adabi daji ne ba a yi masa ƙyaure- Khalid Imam

Ƙagaggen rubutu tamkar ɗa ne wajen mahaifinsa Adabi, shi ko adabi daji ne ba a yi masa ƙyaure- Khalid Imam

Waka saƙa ta ake yi kamar tabarmar kaba, shi kuma zube gina shi ake kamar yadda ake gida - Khalid Daga AISHA ASAS Shahararre kuma sanannen marubuci da ake alfahari da shi a duniyar Adabin Hausa Khalid Imam, ya samu damar amsa gayyatar jaridar Manhaja inda masu karatu za su ji cikaken tarihi tare da nasarorin da ya samu a duniyar rubutu. An dai ce waƙa a bakin mai ita za ta fi zaƙi, ku biyo mu don jin wane ne Khalid Imam: Masu karatu za su so jin tarihin ka.Suna na Khalid lmam. An haife ni a shekarar 1973…
Read More
Muhimmancin aure a addinin Musulunci da rawar da iyaye za su taka akan tarbiyyar yara (2)

Muhimmancin aure a addinin Musulunci da rawar da iyaye za su taka akan tarbiyyar yara (2)

Daga BASHIR ABDULLAHI EL-BASH A mafi yawan lokuta iyaye ba sa zama su tattauna da ’ya’yansu, domin gano halaye da ɗabi'un waɗanda su ke son aura. Daɗi da ƙari, a mafi yawan lokuta zaɓin iyaye bai cika gamsar da ’ya’ya ba wanda hakan ke haifar da matsalolin da ke haddasa mutuwar aure da dama. Ya na da kyau iyaye su na zama da ’ya’yansu su yi magana da su tunda farko su gano abin da su ke so a ba su dama su yi magana da wanda ake son aura musu su fahimci juna kafin kaiwa ga batun aure. Ya…
Read More
Wake ɗaya ɓata gari: Allah sarki ’yar jarida!!!

Wake ɗaya ɓata gari: Allah sarki ’yar jarida!!!

Daga KWAMRED IBRAHIM ABDU ZANGO Akwai wata ’yar jarida wacce ta koyi aikin jarida a wata kafa ta rediyo da wani hamshaƙin ɗan jarida ya koya mata, wato aikin jaridar rediyo. Kullum ka je za ka same ta a ƙasa, shi kuma yana kan kujera! Ya kan ba su damar hirar siyasa da irin ’yan siyasar baka ɗin nan. Ta haka waccan ’yar jarida ta koyi yadda ake hira ta cikin radiyo! Ni a tunanina gani nake cewa, a makaranta ake koyar da wannan babbar sana’a ta jarida tunda akwai fannin wani darasi da ake kira Maskom, wato ‘Mass Communication’.…
Read More
Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Manufar noma a Arewa: Hannunka mai sanda da gwamnati ke ta yi

Tun lokacin zuwan gwamnatin wannan lokaci a shekara ta 2015 ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, ta karkata manufar tattalin arzikin Nijeriya kusan kacokan daga ɓangaren ɗanyen mai zuwa kan harkokin noma, inda gwamnatin ta buɗe wuta wajen ingaza dukkan wani sha’ani da yake da alaƙa da fannin noma ta fuskar ɗaukar matakai daban-daban. Gwamnatin Buhari ta samar da shirye-shirye da tsare-tsare kala-kala, domin cimma wannan buri kama daga ƙarfafa samar da rance mai sauƙi ga manoma zuwa ba su tallafin noma. Haka nan gwamnatin ta kuma tabbatar da rufe iyakokin qasar da hana shigo da shinkafa, wanda hakan ya bai…
Read More
Sojoji sun ragargaji ‘yan Boko Haram a Barno

Sojoji sun ragargaji ‘yan Boko Haram a Barno

Daga WAKILINMU Mayaƙan Boko Haram a Jihar Barno sun kwashi kashinsu a hannu bayan da Dakarun 'Operation Lafiya Dole' wanda a yanzu suke kan aiwatar da 'Operation Tura Takaibango' a yankunan Dikwa da Gulumba Gana, tare da haɗin gwiwar sojojin sama suka fatattake su Daraktan Hulɗa a Jama'a na sojojin, Brigadier General Mohammed Yerima shi ne ya bayyana haka. General Yerima ya ce 'yan ta'addan sun yi amfani da wasu motocin yaƙi ne wajen kai wa yankunan da lamarin ya shafa hari a Lahadin da ta gabata, kuma a daidai lokacin da jama'a ke shirye-shiryen buɗa bakin azumin wannan rana.…
Read More
Sufeto Janar ya bada umarnin janye manyan jami’an ‘yan sanda daga EFCC

Sufeto Janar ya bada umarnin janye manyan jami’an ‘yan sanda daga EFCC

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Riƙo na Rundunar 'Yan Sanda na Ƙasa, Usman Baba, ya bada umarnin janye manyan jami'an 'yan sanda da aka tura aiki a Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Umarnin na ƙunshe ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 15, Afrilu, 2021 wadda Usman Baba ya aike wa shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa. Wasiƙar wadda ta samu sa hannun Idowu Owohunwa babban jami'i na rundunar, ta nuna manyan jami'an 'yan sanda daga kan muƙamin CSP da aka tura aiki a EFCC, ana buƙatar su koma babban ofishin rundunar…
Read More
Gwamna Abiodun ya roƙi JUSUN ta janye yajin aikin da take yi

Gwamna Abiodun ya roƙi JUSUN ta janye yajin aikin da take yi

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, ya yi kira ga Ƙungiyar Ma'aikatan Fannin Shari'a ta Ƙasa (JUSUN) da ta duba sannan ta janye yajin aikin da ta tsunduma tun 6 ga Afrilu, 2021. Idan dai za a iya tunawa, mambobin JUSUN sun shiga yajin aikin gama gari ne domin neman a aiwatar da cin gashin kai ga fannin shari'a game da sarrafa kuɗaɗe kamar yadda kudin tsarin mulki ya amince da shi. Gwamnan ya yi wannan kira ne a lokacin da shugabannin JUSUN reshen jihar Ogun suka ziyarce shi a fadar gwamnatin jihar ƙarkashin jagorancin Mr Afolabi…
Read More