Editor

9387 Posts
Neja: PDP ta dakatar da Babangida Aliyu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Neja: PDP ta dakatar da Babangida Aliyu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Daga AISHA ASAS Jam'iyar PDP a Jihar Neja ta bayyana dakatar da Tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dakta Mu'azu Babangida Aliyu. PDP ta Ƙaramar Hukumar Chanchaga ta dagatar da Aliyu ne bisa wasu zarge-zarge a kansa ciki har da haifar da rashin jituwa a tsakanin shugabannin jam'iyyar. Kazalika, an zargi Tsohon Gwamnan da yi wa jam'iyya zagon-ƙasa, sai batun rashin martaba faɗar Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai, wanda ya buƙaci a haɗu a gudanar da babban taron jam'iyya na jiha. Haka nan, akwai zargin cewa Dr Mu'azu Babangida Aliyu ya tallafa wa APC da kuɗi Naira milyan N450 yayin zaɓen…
Read More
Filato: Gobara ta yi ta’asa a kasuwar doya a Qu’an Pan

Filato: Gobara ta yi ta’asa a kasuwar doya a Qu’an Pan

Daga WAKILINMU An samu aukuwar mummunar gobara a kasuwar doya ta Namu ta Tsakiya da ke yankin Ƙaramar Hukumar Qu'an Pan, Jihar Filato. Manhaja ta kalto cewa gobarar ta auku ne da daddare a Lahadin da ta gabata inda ta lalata tarin doya da sauran kayayyakin abincin na muƙudan kuɗaɗe. Sai dai ya zuwa haɗa wannan labari, jaridar Daily Nigerian ta ce ba a kai ga gano sababin faruwar gobarar ba. Bayanai daga yankin sun nuna sama da manona 100 ne ibtila'in gobarar ya shafa. Tare da yin kira ga gwamnati a matakai daban-daban da su tallafa wa waɗanda lamarin…
Read More
NAFDAC ta gargaɗi ‘yan Nijeriya kan amfani da jabun shayi

NAFDAC ta gargaɗi ‘yan Nijeriya kan amfani da jabun shayi

Daga WAKILINMU Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna (NAFDAC), ta yi jan hankali ga 'yan Najeriya game da wani jabun shayi da ake sayarwa wanda aka ce yana maganin ciwon sukari. Hukumar ta gargaɗi 'yan nijeriya da su guji yin amfani da 'insulin tea' wanda ko rajista bai da shi balle kuma ingancin warkar da wata cuta. Shugabar NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye ce ta yi wannan gargaɗi a wata sanarwar manema labarai da ta fitar a Lahadin da ta gabata a Abuja. Adeyeye ta buƙaci duk inda aka ga ana sayar da wannan shayi na 'insulin tea' a gaggauta…
Read More
Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Daga FATUHU MUSTAPH Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya danganta matsalar tsaron Nijeriya da rashin aikin yi ga matasa, inji wata sanarwa da Waziri Adamawa ya fitar a Lahadin da ta gabata. Atiku ya ce bai taɓa jin wata damuwa ba da faɗin abin da shi ne daidai. Yana mai cewa duba da rahoton da Bloomberg Business ta fitar a Asabar da ta gabata, cewa Nijeriya za ta zama ƙasar da ta fi kowace yawan marasa aiki a faɗin duniya inda yanzu adadin narasa aikin ya kai kashi 33 cikin 100. "Wai yaya aka yi Nijeriya ta kai…
Read More
Musabaƙa: Ganduje ya gwangwanje Gwarzo da Gwarzuwa da kyautar milyan N5

Musabaƙa: Ganduje ya gwangwanje Gwarzo da Gwarzuwa da kyautar milyan N5

Daga UMAR M. GOMBE An kammala Musabaƙar Karatun Ƙur'ani ta Ƙasa karo na 35 a Kano tare da Muhammad Auwal Gusau daga jihar Zamfara a matsayin wanda ya zama gwarzo a ɓangare maza, yayin da Nusaiba Shu’aibu Ahmed daga Kano, ta zama gwarzuwa a ɓangaren mata. Albarkacin bajintar da suka nuna a yayin gasar ya sa Gwamnatin Kano ta yi wa jaruman biyu kyautar kuɗi ta Naira milyan N2.5 ga kowannensu. Da yake jawabi a wajen rufe gasar Asabar da ta gabata, Gwamnan Jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, a bisa wakilicin mataimakinsa Dr Nasiru Yusuf Gawuna, ya ce maza…
Read More
Hajjin 2021: NAHCON ta umurci jihohi su yi wa maniyyatansu rigakafin korona

Hajjin 2021: NAHCON ta umurci jihohi su yi wa maniyyatansu rigakafin korona

Daga AISHA ASAS Hukumar Hajji ta Nijeriya (NAHCON) ta ce ta samu wasiƙa daga Hukumar Bunƙasa Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA) tare da neman NAHCON ta bai wa duka Hukumomin Kula da Walwalar Alhazai na jihohin ƙasar nan 36 su yi wa maniyyatansu allurar rigakafin korona. A wata takardar sanarwa wadda Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike da Yaɗa Labarai na NAHCON, Sheikh Suleman Momo Imonikhe ya sanya hannu a ranar Lahadi, hukumar ta buƙaci ɗaukacin Hukumomin Kula da Walwalar Alhazai na jihohin ƙasar nan da su hanzarta yi wa baki ɗayan maniyyatansu allurar rigakafin korona. A cewar NAHCON yin allurar a kan…
Read More
Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu mai zamanta a Akure babban birnin jihar Ondo, ta umarci rundunar 'yan sandan jihar da ta biya diyyar Naira milyan N100 ga Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Agboola Ajayi. Laifin da ya haifar wa 'yan sandan hukuncin biyan diyyar shi ne, a ranar 20, Yuni, 2020 'yan sandan sun hana mataimakin gwamnan jihar na wancan lokaci, wato Agboola Jayi, fita daga Fadar Gwamnatin jihar wajajen ƙarfe 7 na dare, haka ma abin ya sake faruwa washe gari 21, Yuni, 2020 da misalin ƙarfe 9 na safe, bisa zargin cewa Ajayi na take-taken ficewa daga jam'iyyar APC.…
Read More
Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ce farfaɗo da yankin Tabkin Chadi zai taimaka wajen sassauta matsalar neman ƙetarawa zuwa Turai da matasa kan yi ta hanyar ketawa ta sahara. Buhari ya bayyana haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncin takwaransa na Chadi,  Marshal Idris Deby a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Asabar. A cewar Buhari, kimanin mutane milyan 30 ne matsalar tsukewar Tabkin Chadi ta shafa wanda a yanzu kashi 10 cikin 100 na girman tabkin ne ya yi saura idan aka kwatanta da asalin girmansa, inji sanarwar da mai magana da yawun shugaban,…
Read More
Shirye-shiryen Zuwan Ramadan

Shirye-shiryen Zuwan Ramadan

Daga IMAM YAHYA ALYOLAWI Kalmar Ramaḍan an tsago ta ne daga Kalmar “Ramad”, wadda ke nufin abin da ya duku da zafin rana. Larabawa kan kira tumakin da suka sha zafin rana a wajen kiwo da suna ‘ramidah’, zafin ranar da har kan yi sanadin lalacewar hantar dabbobin saboda tsananin zafi. Watan Ramadan ya samu sunansa ‘Ramadan’ ne saboda ƙona zunuban bayin Allah na gaskiya da yakan yi. Imām Qurtubi ya ce: ''Ramadan ya samu sunansa ne saboda ƙona kurakuran bayin Allah nagartattu da yake yi.” Abu Huraira (RA) ya ruwaito Annabi (SAW) na cewa: "Duk wanda ya azumci watan…
Read More