11
Mar
Daga FATUHU MUSTAPHA Wata tawagar lauyoyi a jihar Kano ta yinƙura neman haƙƙinta daga hannun jam'iyyar APC reshen jihar na aikin da ta yi mata yayin zaɓen 2019. A wata wasiƙa da suka aika wa APC ta hannun lauyansu Usman Umar Fari, lauyoyin da lamarin ya shafa sun buƙaci jam'iyyar ta hanzarta biyansu kuɗeɗen aikin da suka yi mata yayin babban zaɓe na 2019. Lauyoyin sun ce kuɗin da suke nema a biya su, haƙƙin aikin da suka yi wa APC ne kan batutuwan da suka shafi sha'anin shari'ar zaɓe. Lauyan lauyoyin, Usman Fari, ya ja hankalin jam'iyyar kan cewa…