Editor

9276 Posts
Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Daga FATUHU MUSTAPHA Wata tawagar lauyoyi a jihar Kano ta yinƙura neman haƙƙinta daga hannun jam'iyyar APC reshen jihar na aikin da ta yi mata yayin zaɓen 2019. A wata wasiƙa da suka aika wa APC ta hannun lauyansu Usman Umar Fari, lauyoyin da lamarin ya shafa sun buƙaci jam'iyyar ta hanzarta biyansu kuɗeɗen aikin da suka yi mata yayin babban zaɓe na 2019. Lauyoyin sun ce kuɗin da suke nema a biya su, haƙƙin aikin da suka yi wa APC ne kan batutuwan da suka shafi sha'anin shari'ar zaɓe. Lauyan lauyoyin, Usman Fari, ya ja hankalin jam'iyyar kan cewa…
Read More
Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Daga WAKILINMU Majalisar Wakilai ta Ƙasa, ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta maida kuɗaɗen da Ibori ya sata, Pan milyan  £4.2, ga Jihar Delta. Wannan ya biyo bayan ƙudirin da 'yan majalisar daga jihar Delta suka gabatar wa majalisar ne a Larabar da ta gabata. Haka nan, 'yan majalisar sun ce jimillar kuɗin Pan miliyan £6.2 ne amma ba milyan  £4.2 ba kamar yadda aka ruwaito. Bugu da ƙari, Majalisar ta buƙaci Ma'aikatar Kuɗi ta Kasa da ta bai wa Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari'a, Abubakar Malami, umarnin ya miƙa wa Majalisar dukkan takardun da ke da alaƙa da…
Read More
Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Nasarawa Engineer Abdullahi Sule, ya ƙaddamar da allurar rigakafin cutar koron inda shi da mataimakinsa, Dr. Emmanuel Akabe, suka soma yin rigakafin na Oxford-AstraZeneca. Bikin ƙaddamarwar ya gudana ne ranar Talata a fadar gwamnatin jihar da ke Lafia, babban birnin jihar. Da yake yi wa manema labarai bayani jim kaɗan bayan ya yi allurar, Gwamna Sule ya yi kira ga 'yan jiharsa, musamman ma waɗanda suka fi fuskantar haɗarin harbuwa da cutar kamar 'yan siyasa da sarakunan gargajiya da sauransu, da su tabbatar sun yi allurar. Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen nuna godiyarsa…
Read More
Shari’ar Maina: Kotu ta gayyaci Malami da Magu don su bada shaida

Shari’ar Maina: Kotu ta gayyaci Malami da Magu don su bada shaida

Daga UMAR M. GOMBE Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta bada sammaci wanda ya tilasta wa Babban Lauyan Tarayya (AGF), Abubakar Malami SAN, da tsohon shugaban riƙo na hukumar EFCC Ibrahim Magu, da su bayyana a gabanta. Kotu ta buƙaci ganin waɗanda lamarin ya shafa ne domin su bada shaida a shari’ar cin hanci da rashawa da ake yi wa tsohon shugaban kwamitin gyaran fansho, Abdulrasheed Maina. Kazalika, kotun ta umarci Shugaban Babban Bankin Ƙasa (CBN), Godwin Emefiele da wasu da su bayyana a gabanta a ranakun 9, 10 da 11 na Maris domin bada shaida. Sauran mutanen da…
Read More
Ta hannun gwamnati kaɗai za a shigo da rigakafin korona, cewar Mamora

Ta hannun gwamnati kaɗai za a shigo da rigakafin korona, cewar Mamora

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta ce ba ta yarda 'yan kasuwa su shigo da allurar rigakafin cutar korona ba, tare da cewa dole dukkan rigakafin da za a shigo da su ya kasance ta hannun gwamnati. Ƙaramin Ministan Lafiya, Olorunnimbe Mamora ya faɗi haka ran Talata a Abuja.Ministan ya ce 'yan Nijeriya masu bukatar a yi musu rigakafin korona sai su yi rajista a shafin intanet na Hukumar Kula da Lafiaya a Matakin Farko. Mamora ya ce a halin yanzu ba a yarda 'yan kasuwa su soma harkar shigo da allurar rigakafin korona ba. Ya ce gwamnati ba za…
Read More
Baƙin haure 39 sun mutu a Tunisia

Baƙin haure 39 sun mutu a Tunisia

Daga FATUHU MUSTAPHA Aƙalla baƙin haure 39 ne suka rasa rayukansu a lokacin da kwale-kwale biyu suka nitse a kusa da Tunisia a ranar Talata yayin da suke ƙoƙarin tsallake kogin Bahar Rum zuwa tsibirin Lampedusa na Italiya, in ji jami'an tsaron Tunisia. Jami'in Tunisa Mohamed Zekri, ya ce masu tsaron bakin ruwa sun samu nasarar ceto wasu mutum 165, sannan ana ci gaba da neman ƙarin waɗanda suka tsira a gaɓar Sfax. Ya ƙara da cewa dukkan baƙin hauren da suka mutun 'yan Afirka ne. Jaridar Alarabiya ta ruwaito cewa, a 2019 kimanin baƙin haure 'yan Afirka su 90…
Read More
EFCC ta cafke ‘yan damfara 37 a Ekiti

EFCC ta cafke ‘yan damfara 37 a Ekiti

Daga WAKILINMU Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arzikin Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC) ta cafke wasu matasa 37 da aka fi sani da 'yahoo-yahoo boys' bisa zargin aikata damfara a intanet a Ado-Ekiti, jihar Ekiti. Hukumar da kanta ta bayyana hakan a wata sanarwar manema labarai da ta fitar ta hannun Shugaban Sashen Yaɗa Labaranta, Wilson Uwujaren, a Litinin da ta gabata. Sanarwar ta nuna EFCC ta yi nasarar kama matasan ne biyo bayan bayanan sirri da ta tattara kan harkokinsu na damfarar mutane ta intanet a yankin. Hukumar ta ce sakamakon binciken da jami'anta suka gudanar a…
Read More
Ogun ta samu rigakafin korona guda 100,000

Ogun ta samu rigakafin korona guda 100,000

Daga AISHA ASAS A Litinin da ta gabata Gwamna jihar Ogun, Dapo Abiodun, ya karɓi allurar rigakafin cutar korona na AstraZeneca/Oxford guda dubu 50,000 a matsayin gudunmuwa daga Gwamnatin Tarayya. Maganin ya shiga hannun gwamnan ne a ofishinsa da ke Abeokuta, jim kaɗan bayan dawowar tawagar da ta wakilci jihar ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Lafiya na jihar, Dr Tomi Coker. Gwamnan ya shaida wa manema labarai cewa Ogun ita ce jiha ta farko da ta soma karɓar rigakafinta. Yana mai cewa allura ƙwaya 50,000 da ta samu rukunin farko ne na abin da take sa ran samu baki ɗaya. Ya ce…
Read More