29
Apr
Daga BASHIR ISAH Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja, ya ce kafa Jami'ar Edusoko zai taimaka wajen magance ƙalubalen samun gurbin karatu da ake fama da shi a jihar Neja. Gwaman ya bayyana haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncin Kwamitin Amintattu na Jami'ar Edusoko ƙarkashin jagorancin Etsu Nupe, Alhaji Yahaya Abubakar, a fadar gwamnatin jihar da ke Minna. Ya ce akwai ɗimbin ɗalibai a jihar Neja da ke neman gurbin karatu a jami'a, yana mai cewa zuwan Jami'ar Edusoko zai zama mafita ga ɗaliban. Baya ga yaba wa Etsu Nupe bisa ƙoƙarin samar da wannan jami'a, Gwamna Bello…
