Editor

9513 Posts
Buhari ya yi na’am da sabon tsarin albashin fansho mafi ƙaranci

Buhari ya yi na’am da sabon tsarin albashin fansho mafi ƙaranci

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yarda a biya masu karɓar fansho da sabon tsarin albashi mafi ƙaranci. Sakatariyar Hukumar Fansho, Dr Chioma Ejikeme, ita ce ta bayyana haka yayin taron manema labarai a Abuja a Juma'ar da ta gabata. Jami'ar ta ce da wannan amincewar da aka samu daga wajen Shugaban Ƙasa, an ƙarfafa wa kwamitin PTAD kan ya soma gyare-gyare game da abin da ake biyan masu karɓar fansho domin ya daidaita da sabon tsarin biyan haƙƙoƙin nasu. Ejikeme ta ce sabon tsarin biyan fansho ɗin zai soma aiki ne daga Mayu, 2021. Ta kara da…
Read More
Kadafur ya zama muƙaddashin gwamnan Barno na kwana 21

Kadafur ya zama muƙaddashin gwamnan Barno na kwana 21

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Dokokin Jihar Barno ta amince da buƙatar Gwamna Babagana Umara Zulum inda ya nemi a naɗa mataimakinsa, Umar Usman Kadafur, a matsayin mauƙaddashinsa. Zulum ya miƙa wannan buƙata ga majalisar ne domin ba shi zarafin tafiya hutu na kwana 21, kama daga ranar 29 ga Afrilu zuwa 19 ga Mayu, 2021. Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Abdulkarim Lawan, ya ce tun a ranar 23 ga Afrilun da ya gabata gwamnan ya miƙa wa majalisar wasiƙar wannan buƙatar tasa, yana mai neman majalisar ta ba shi damar tafiya hutu na kwanaki 21. Kazalika, Shugaban Majalisar ya ce…
Read More
Gwamnatin Neja ta sauya wa ‘yan gudun hijira 3500 sansani

Gwamnatin Neja ta sauya wa ‘yan gudun hijira 3500 sansani

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Neja ta sake wa wasu 'yan gudun hijira a jihar su 3500 matsuguni zuwa Gwada Model Primary School a Juma'ar da ta gabata. Waɗanda lamarin ya shafa 'yan gudun hijira ne daga yankunan da 'yan fashin daji da Boko Haram suka ɗaiɗaita a jihar kwanan nan. A bayanin Gwamna Sani Bello ta bakin Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar (NSEMA), ya bada umarni a tabbatar 'yan gudun hijirar na samun kulawar da ta dace na zaman da za su yi a sabon sansanin nasu har zuwa lokacin da komai zai daidaita kana a maida kowa…
Read More
Akwai bambanci ƙwarai tsakanin rubutun zube da na jarida – Mairo Muhammad Mudi

Akwai bambanci ƙwarai tsakanin rubutun zube da na jarida – Mairo Muhammad Mudi

*Ba na zayyana labari irin na abinda ake cewa ‘mijin novel'- Mairo Mudi Daga AISHA ASASSanannen abu ne marubuta sun karkasu daban-daban, inda za ka samu wani ya fi ƙwarewa a rubutun waƙe, ko zube ko kuma wasan kwaikwayo da sauran su, duk da haka akwai wasu tsiraru daga cikin marubuta da aka ba su baiwar shiga kowane ɓangare na Adabi su taka rawar da za a yaba masu. Irin waɗannan marubuta dai su na da karanci domin ba kasafai ake samun su ba. Waɗannan marubuta sun kasance gwanaye a kowane ɓangare na rubutu har a kasa gane wane fage…
Read More
Me ya sa soyayya ke mutuwa bayan Aure?

Me ya sa soyayya ke mutuwa bayan Aure?

Daga AMINA YUSUF ALI Kamar yadda muka sani ko muke iya gani, yawancin aurarrakin yanzu ana dasa su ne bisa soyayya. Wannan abu haka yake musamman a al'ummar Hausa. Da shuɗewar zamani da ilimi har ma da wayewa sun sa an kusa ma a manta a ana auren dole. Amma abu mafi mamaki shi ne, bayan an yi auren soyayyar wacce kamar a haɗiye juna. Sai kuma wasu abubuwa na rashin jituwa su vullo, a rasa ma gane kan zaman nasu. A haka idan ba a kai zuciya nesa ba, sai rabuwa. Ko kuma idan ba a rabun ba, a…
Read More
Ina mafita ga matsalolin Arewa?

Ina mafita ga matsalolin Arewa?

Daga AMINU ƊANKADUNA AMANAWA Arewa yanki ne daga cikin yankunan dake akwai a dunkulalliyar kasa da turawan mulkin mallaka suka hade yankunan kudu da Arewa waje daya da yanzu muke a ciki da kuma tinkaho da ita ta Nijeriya. Duk da yake ko a arewar ta kasu a yankuna daban-daban, kama daga arewa maso gabas, yamma, dama tsakkiya, yankin na fuskantar kalubalai da tarin matsalolin dake kokarin mayar da yankin saniyar ware. Matsalolin da suka tashi daga talauci da kusan ke akwai a lunguna da sako na jihohi, zuwa na tsaro da ya zama ruwan dare, garkuwa da mutane domin…
Read More
Inuwa Ibrahim Waya da tsatsonsa a mahangar tarihi: Kaza da tone-tone?

Inuwa Ibrahim Waya da tsatsonsa a mahangar tarihi: Kaza da tone-tone?

Daga KWAMRED IBRAHIM ABDU ZANGO Siyasa wata aba ce wacce ake yin ta domin kyautata wa al’umma a kowacce ƙasar duniya, wacce ake yin zaɓe, domin mulki irin na zamani. Gaskiya kamar yadda tarihi ya nuna an fara salon wannan mulki tun tale-tale, kususan a can wata ƙasa wacce ita ce farkon bayyanar Turawan duniya. Haka dai abin yake kuma a wancan duniyar Turawa wacce ita ce ta buɗewa dukkan duniya harkar dimukraɗiyya, wacce yanzu ta haɗe duniya kaf ɗinta. Duk da cewa waccan ƙasa ita ce farko, amma mun karanta tarihinta a makaranta wadda har rumawa suka rungume ta…
Read More
Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Tsaro: Gwamnonin Arewa na da rawar takawa

Duk da matsayin da jihohin yankin Arewacin Nijeriya suka samu kawunan su a cikin shekaru 16 da su ka shuɗe har zuwa yanzu da gwamnatin APC ke mulkin ƙasar, alamuran yankin suka shiga taɓarɓarewa, harkar tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma ya kau, kusan kowane ƙauye su na fama da ruɗani masu garkuwa da mutane, don amsar kuɗin fansa, su na fama da hare-hare da rigingimun makiyaya. Gwamnonin da haƙƙin hakan kuma ya rataya a wuyan su ba su taɓuka ba, don ɗaukar wani mataki, walau na gaggawa ko wanda aka tsara na musamman, don magancewa. Haka nan su na ji,…
Read More
Wata Guguwa

Wata Guguwa

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM Bayan fargaba da asarar rayuka da dunkiyoyi da annobar kwarona ta haddasa, rayuwa ta fara dawowa daidai a wasu wurare da dama, harkoki sun fara komawa kamar yadda aka san su. Farkon ɓullar wannan cuta mutane da dama ba su ɗau abin da muhimmanci ba, tunanin kowa shine cutar za ta tsaya ne a iyakar inda ta ɓulla kamar yadda aka saba, abu kamar wasa sai ga ta ta game duniya gabaɗaya ta buwayi duniya har ta illata tattalin arzuƙin mutane da ƙasashe da dama musamman ƙasashe masu tasowa da kuma talakawanta. Har yanzu ba wai…
Read More
Za mu tsige Buhari muddin magance matsalar tsaro ya faskara – Hon Bagos

Za mu tsige Buhari muddin magance matsalar tsaro ya faskara – Hon Bagos

Daga AISHA ASAS Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar shiyyar Jos ta Kudu da Jos ta Gabas a Majisar Wakilai ta Ƙasa, Dachung Bagos, ya ce majalisa za ta ɗauki matakin tsige Shugaba Muhammadu Buhari muddin Majalisar Zartarwa ta Kasa ta kasa kawo ƙarshen matsalolin tsaron da suka addabi ƙasa. Ɗan majalisar ya yi wannan furuci ne yayin wani shiri da aka yi da shi a wannan Alhamis ɗin a tashar talabijin ta Channels. Idan dai za a iya tunawa, ko Larabar da ta gabata sai da majalisar ta kafa wani kwamiti na mutum 40 tare da ɗora masa aikin binciko…
Read More