05
Apr
Daga FATUHU MUSTAPHA Fitaccen malamin Islman nan na Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi wata ganawar sirri tare da Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo a gidansa da ke Abeokuta babban birnin jihar Ogun, a Lahadin da ta gabata. Wata majiya ta kusa da taron, ta ce Gumi ya zaɓi ganawa da Chief Obasanjo ne kasancewarsa na mai faɗa a ji a cikin ƙasa kuma wanda al'umma ke girmamawa. Malamin ya labarta wa Obasanjo ziyarar da ya kai wa Fulani masu fashi a Arewacin ƙasa da zummar gwamnati ta yi wa yanayin kyakkyawar fahimta da kuma yin aiki da shawarwarin da…