Editor

9513 Posts
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata kimanin 300 a Zamfara

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga Jihar Zamfara, sun nuna cewa 'yan bindiga sun sace ɗalibai mata kusan su 300 a Makarantar Sakandaren Gwamnati (GSS) Jangeɓe, da ke yankin ƙaramar hukumar Talata-Mafara a jihar, a tsakar daren Juma'a. Kwamishinan Labarai na jihar, Malam Suleiman Tunau Anka, ya tabbatar wa manema labarai faruwar haka, inda ya ce 'yan bindiga sun shiga makatar ne da misalin ƙarfe 1 na tsakar daren Juma'a suka kwashi ɗalibai. Sai dai Anka bai faɗi adadin ɗaliban da lamarin ya shafa ba. Wannan na faruwa a daidai lokacin da Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle, ya yi kira ga…
Read More
EFCC ta yi sabon shugaba

EFCC ta yi sabon shugaba

Daga FATUHU MUSTAPHA A Larabar da ta gabata Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin sabon Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Sanatocin sun shafe sa’o’i biyu suna tantance Bawa kafin daga bisani suka tabbatar da shi a sabon matsayin nasa. Yayin da ake tantance shi, Bawa ya bai wa majalisar tabbacin cewa zai yi aiki tukuru don gyara wa hukumar zama ta hanyar inganta harkokinta kafin ƙarewar wa’adin jagorancinsa. Bawa ya ce zai yi aiki tare da waɗanda suka dace a sassan duniya domin tabbatar da Nijeriya ta…
Read More
Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Bello ya rattaba hannu a wasu sabbin dokokin jiharsa

Daga AISHA ASAS Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya sanya wa wasu sabbin dokoki guda biyu hannu. Dokokin su ne, dokar gudanar da binciken sanin lafiyar masu shirin yin aure kafin ƙulla aure da kuma dokar haramta tada hankalin jama'a da abin da ya jiɓanci haka. Taron sanya wa dokokin hannu ya gudana ne a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Minna. Da yake jawabi bayan kammala sanya wa dokokin hannu, Gwama Bello ya bayyana dokokin a matsayin masu muhimmancin gaske. Bello ya yaba wa Majalisar Dokokin jihar bisa ƙoƙarin da ta yi wajen nazarin dokokin yadda ya dace har…
Read More
Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Myanmar: An yi arangama tsakanin magoya bayan sojoji da ɓangaren Suu Kyi

Rahotanni daga Ƙasar Myanmar sun nuna cewa, magoya bayan sojin da suka yi juyin mulki a ƙasar sun yi arangama da masu adawa da kifar da gwamnatin Aung San Suu Kyi a birnin Yangon, yayin da hukumomi suka daƙile ɗalibai a makarantunsu don hana su zanga-zanga. Tun lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a ranar 1 ga Fabairu, tare da tsare Suu Kyi, ƙasar ta tsunduma cikin tashin hankali. Kimanin makonni uku kenan da ake gudanar da zanga-zanga a kowacce rana da kuma yajin aiki a ƙasar. Sai dai ‘yan sanda sun rufe ƙofofin makarantun da nufin hana ɗarruruwan…
Read More
FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

FIAN ta nuna takaicinta kan yadda ƙungiyoyi kan gaza kula da ‘yanwasa

Ƙungiyar Masu Shiga-tskanin Harkokin Ƙwallon Kafa ta Kasa (FIAN), ta nuna damuwarta kan yadda masu ruwa da tsaki kan harkokin ƙwallon ƙafa ba su ɗaukar lamarin 'yan ƙwallon da muhimmanci wajen biyan albashinsu da alawus-alawus da makamantansu yadda ya dace. Shugaban FIAN na ƙasa, Ayodele Thomas, ya nuna damuwarsa kan yadda masu ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa suke nuna halin ko-in-kula wajen kula da sha'anin 'yan wasansu yadda ya kamata. Da yake zantawa da manema labarai, Thomas ya ce abin takaici ne yadda masu kulob-kulob kan gaza wajen lura da 'yan ƙwallonsu bilhaƙki. Ya ce kamata ya yi kafin ƙungiya ta ɗauki…
Read More
Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Abuja: An yi jana’izar mayaƙan sama da suka rasu a haɗarin jirgin sama

Daga BASHIR ISAH An gudanar da jana'izar jami'an sojin saman nan su 7 da suka rasu a haɗarin jirgin sama da ya auku a Abuja a Lahadin da ta gabata. Jami'an da lamarin ya shafa sun cim ma ajalinsu ne bayan da jirginsu, ƙirar Beechcraft King Air 350, ya faɗo a ƙauyen Bassa daura da Babban Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe, bayan da suka tashi da nufin zuwa aiki a jihar Neja. Mai Magana da Yawun Rundunar Sojin Sama na Nijeriya, Air Vice Marshal Ibikunle Daramola ya ce jirgin ya fuskanci matsalar inji kafin aukuwar haɗarin. Cikin waɗanda suka…
Read More
An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

An sako direban Adamawa United da aka yi garkuwa da shi

Daga WAKILIN MU An sako direban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Adamawa United wanda aka yi garkuwa da shi a ranar Asabar da ta gabata. An yi garkuwa da direban ƙungiyar ne a lokacin da suka faɗa hannun wasu 'yan fashi da makami a kan hanyarsu ta zuwa birnin Legas don buga wasan da aka tsara musu a can. Yazu haɗa wannan labari, babu wani cikakken bayani a kan ko sai da aka biya diyya kafin aka saki direban. Tun farko, 'yan fashin sun buƙaci a biya diyyar naira milyan N50 kafin su saki direban da suka yi garkuwa da shi,…
Read More
Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Saudiyya: Zaki Yamani ya rasu

Daga FATUHU MUSTAPHA Allah Ya yi wa fitaccen tsohon Ministan Harkokin Mai na Saudiyya, Ahmed Zaki Yamani, rasuwa. Yamani ya rasu ne a wata asibitin Landa a Litinin da ta gabata. Wata 'yar marigayin mai suna Mai Yamani, ta ce matsalar zuciya ce ta yi ajalin mahaifin nata, inda ya rasu yana da shekara 90. Yamani na ɗaya daga cikin mutanen da ƙasar Larabawa ba za ta mancewa da su ba saboda irin rawar da ya taka wajen cigabanta. A halin rayuwarsa, marigayin ya yi tsayin daka wajen bunƙasa harkokin mai na ƙasar Saudiyya. A matsayinsa na ministan albarkatun mai…
Read More
Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Majalisa ta tabbatar da naɗin sabbin jakadu duk da ƙorafin da aka yi a kan su

Daga WAKILIN MU Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin tsoffin Shugabannin Tsaron Nijeriya a matsayin jakadu. Wanna ya faru ne a Talatar da ta gabata. Idan ba a manta ba, a Janairun da ya gabata Shugaba Buhari ya zaɓi General Abayomi G. Olonisakin da Lt. General Tukur Y. Buratai da Vice Admiral Ibok-Ete E. Ibas da kuma Air Marshal Sadique B. Abubakar don zama jakadun Nijeriya bayan murabus da suka yi daga aiki ba da jimawa ba. Amincewa da naɗin ya zo ne bayan gamsuwa da majalisar ta yi da rahoton kwamitin majalisar kan harkokin ƙasashen waje ƙarƙashin jagorancin Adamu…
Read More
Kuɗin intanet: Majalisa ta gayyaci shugaban CBN don ya yi ƙarin haske

Kuɗin intanet: Majalisa ta gayyaci shugaban CBN don ya yi ƙarin haske

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya bayyana a gaban Majalisar Dattawa domin kare batun haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet (crypto currencies) da gwamnati ta yi. Majalisar ta gayyaci Emefiele ne domin ya yi mata ƙarin haske kan irin damarmaki da kuma haɗarin da ke tattare da harkar kuɗaɗen intanet ga tattalin arzikin ƙasa. A can baya, Babban Bankin, ta hannun Daraktan Sashen Sanya wa Bankuna Ido Bello Hassan, ya bayyana cewa waɗannan kuɗaɗe na intanet wasu da ba a san ko su wane ne ba suke bada su kuma ba tare da wasu sanannun dokoki ba.…
Read More