Babaji

4788 Posts

Lauyoyi sun ja kunnen Sufeto Janar kan kawo cikas ga zanga-zangar lumana

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Yayin da ake cigaba da shirin zanga-zanga a faɗin Nijeriya, lauyan kare ƴancin Ɗan Adam, Inibehe Effiong ya aika da saƙo ga Sufeto Janar na 'Yan sanda, Kayode Egbetokun inda ya buƙaci a bai wa masu zanga-zangar kariya. Effiong ya ce zanga-zangar lumana a dokar Nijeriya ta halatta, dan haka akwai buƙatar hukumomin tsaro su ba su kariya, ya na mai kafa hujja da sakin-layi na 39 da na 40 na kundin dokar ƙasa. Ya ƙara da kira ga Sufetan, ya umarci dukkan kwamishinoni da ɓangarorin da ke da alhakin bayar da tsaro ga al'umma domin…
Read More

Kotu ta yanke wa ƴan Boko Haram 125 hukunci

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Aƙalla mayaƙan Boko Haram 125 tare da masu ɗaukar nauyinsu ne aka yanke wa hukunci a bainar jama'a a wani zama na kwana biyu a Kainji da ke jihar Nija. An same su ne laifukan ta'addancin kan iyaka, tallafa wa ta'addanci da wasu lafukan kotun fashin ƙasa-da-ƙasa. Antoni Janar na ƙasa kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, shi ne wanda ke sanya ido kan lamarin hukuncin tare da haɗin gwiwar ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro. An gudanar da hukuncin ne a ranakun Talata da Laraba wanda masu shari'a biyar daga babbar kotun…
Read More

Zanga-zangar tsadar rayuwa: Rundunar ‘Yan sanda ta baza jami’ai 4,200 a Abuja

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rundunar 'Yan sandan Abuja ta ɗauki matakin baza jami'ainta a lunguna da saƙo-saƙo na babban birnin sakamakon zanga-zangar tsadar rayuwa da wasu masu ƙishin al'umma da matasa su ka shirya yi a faɗin Nijeriya. Mai magana da yawun rundunar, SP Josephine Edeh ta bayyana hakan wa manema labarai a ranar Juma'a, inda ta ce sun ɗauki matakin bada kariya wa al'umma ta hanyar yin bincike ga masu zanga-zangar a wurare daban-daban da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro. Ta ce, Kwamishinan babban birnin, Benneth Igweh a lokacin da ya ke magana akan damar ƴanci da dokar ƙasa…
Read More

Sai kun cike sharuɗa bakwai kafin ku yi zanga-zanga, Sufeta Janar ga jagorori

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Sufeta Janar na 'Yan sanda, Kayode Egbetokun ya Umarci duk wata tawaga da ke shirin yin zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya su bayar da bayanan da ake buƙata ga kwamishinan Ƴan sandan jihar da za a gudanar da ita. Kayode ya faɗi hakan ne a ranar Juma'a a Abuja inda ya yi kira ga al'umma da su kasance masu lura da hangen nesa kafin shiga kowace irin zanga-zanga dan gujewa haifar da koma baya wa ƙasa. Abubuwan da ake buƙatar bayaninsu daga kowace tawaga ta zanga-zangar sun haɗa da; * hanyoyin da za a bi da…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Bom ya yi sanadiyar mutuwar sojoji shida a Borno

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Sojoji shida sun rasa rayukansu a lokacin da wani abin fashewa ya tarwatsa wata motar soji a Mungunu da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno. Lamarin ya auku ne a ranar Alhamis inda motar jami'an ta haye kan wani bom ake zargin mayaƙan Boko Haram ne su ka dasa a kan hanyar Gamboru Ngala- Maiduguri, kamar 'Sahara Reporters' ta ruwaito. Rundunar sojin ta samu rahoton cewa, mayaƙan sun kai hari wani gari da ke kusa da inda ta ke. Jin haka ke da wuya rundunar ta tura motoci uku domin kai mu su ɗauki wanda hakan…
Read More

Hedikwatar Tsaro da DSS sun fitar da matakan gaggawa kan zanga-zangar tsadar rayuwa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Jami'an tsaro ciki har da hedkwatar tsaro (DHQ) da Ƴan sandan farin kaya (DSS) sun ankarar da jami'ansu kan cewa su kasance cikin shiri domin kaucewa tashin-tashina gani yadda lokacin zanga-zangar tsadar rayuwa na cigaba da ƙaratowa. Hukumomin tsaron sun bayyana hakan ne ta mabanbanta hanyoyi inda suka tabbatar da cewa ba a yi nufin gudanar da zanga-zangar cikin lumana ba. DSS ta ce, babbar manufar waɗanda ke shirya zanga-zangar ita ce a canza gwamnati a matsayin jigo. DHQ ta ce, wani binciken sirri ya nuna cewa akwai alamun a juya zanga-zangar ta koma rikici. Shugaba…
Read More

Rikicin matatar Ɗangote: Majalisar Dattijai ta ayyana ranar tattaunawa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Majalisar Dattijai ta zaɓi watan Satumba a matsayin lokacin tattauna batun rikicin da ke tsakanin kamfanin Ɗangote da kuma ofisoshin gudanarwar man fetur da suka haɗa da hukumar NMDPRA da kamfanin NNPC. Shugaban ƙwarya-ƙwaryar kwamitin da shugaban majalisar, Godswill Akpabio ya naɗa don sasanci, Sanata Bamidele Opeyemi ya faɗi haka, yana mai cewa za su bayyana dukkan waɗanda ke da hannu cikin kawo rigima a ɓangaren harkar mai a Nijeriya. Opeyemi ya bada tabbacin cewa kwamitinsu zai samar da sakamako na abin a zo a gani ba kamar irin na kwamitocin da aka yi a baya…
Read More

An rufe adireshin ɗaukar ma’aikata a NNPC na wucin-gadi saboda cinkoso

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Kamfanin man fetur na Ƙasa, NNPC ya ruwaito cewa adireshinsa na ɗaukar ma'aikata ya rufe sakamakon cinkoson adadin waɗanda ke shigar da bayanan neman aiki. NNPC ya buɗe adireshin ne domin cike gurabe daban-daban a ranar Juma'a wanda za a rufe a ranar 20 ga watan Agusta. Kasancewar masu ziyaratar shafin adireshin sun yawaita, hakan ya sa ya kulle daga karɓar su. Wata sanarwa da kamfanin ya fitar ta kafar X, ta ce tawagar jami'an gudanarwa na ƙoƙarin gyara matsalar wacce a ke fatan magance ta nan ba da jimawa ba. Kazalika, kamfanin ya sake tabbatar…
Read More

Tinubu ya shashantar da maganar zanga-zanga, ya ce ba ita suke tsoro ba, halin da za a jefa talaka ke damun sa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa Majalisar sarakunan gargajiya ta Nijeriya cewa gwamnatinsa ba ta shakkar zanga-zanga, yana mai cewa halin da za a jefa talakawa ke damun sa. Ƙungiyoyin matasa sun shirya zanga-zangar tsadar rayuwa a faɗin Nijeriya da za a yi a ranar 1 ga watan Agusta wanda ake fatan ya zama sababin magance matsalolin al'umma a faɗin ƙasar. Shugaba Tinubu ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke ganawa da sarakunan a Fadar shugaban ƙasa da ke Abuja inda ya ce Nijeriya ta na ƙoƙarin farfaɗowa daga halin da ta tsinci…
Read More

Mata za su shirya zanga-zanga tsirara a Majalisar Dokoki ta Ƙasa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Bayan da aka tsige Sanata Ali Ndume a matsayin Mai Tsawatarwa da kuma Mataimankin shugaban kwamitin daidaito, magoya baya da taron mata daga Kudancin jihar Borno su na shirin gudanar da zanga-zangar lumana a Majalisar Dokoki ta Ƙasa. Koken nasu yana da alaƙa da sauke Ndume daga muƙaminsa da su ka danganta halinsa na rashin yin shuru a Majlisa da kuma caccakar gwamantin Shugaba Tinubu inda suka bada misali da matsalolin yunwa da kuma rashin tsaro. Sanata Ndume ke wakiltar ƙananan hukumomi tara a jihar Borno inda wakilan mazuɓu 101 na mazaɓarsa su ka taru a…
Read More