24
Aug
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Da safiyar ranar Lahadin nan gwamnatin jihar Kebbi ta sanar da rasuwar Alhaji Garba Muhammed Kola da aka fi sani da Kanga. Alhaji Garba Muhammed Kola ya rasu a garin Birnin Kebbi bayan ya yi fama da rashin lafiya.Kafin rasuwar da shi ne shugaban sashen tsare-tsaren wasannin al'adun gargajiya a ma'aikatar yaɗa labarai ta jihar Kebbi. Ya rasu ya bar mata uku da yaya da dama.An kuma yi jana'izar sa a garin Birnin Kebbi kamar yadda shari'ar musulunci ta tanada. Kwamishinan yaɗa labarai Alhaji Ahmed Yakubu Birnin Kebbi da babban Sakatare Alhaji Alkasim Salihu Gunabi…
