Kasuwanci

Nijeriya ta zama ƙasa ta 4 a jerin ƙasashe 10 mafiya amsar bashi a Bankin Duniya

Nijeriya ta zama ƙasa ta 4 a jerin ƙasashe 10 mafiya amsar bashi a Bankin Duniya

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai ƙasar Nijeriya ta taka matsayi na 4 na ƙasashen da suka fi kowa cin bashi a jerin sunayen ƙasashe na IDA na Bankin Duniya (ƙasashe masu yin rance a bankin). A yanzu haka ana bin ƙasar bashin Dalar Amurka biliyan 14.3. Nijeriya ta daɗe a wannan matsayi nata na huɗu a jerin ƙasashe da ke ƙungiyar (IDA) masu rancen. Tun bayan da ta baro matsayi na 5 a Yunin shekarar 2022. Duk da Nijeriya ta kasance mai matsayi na 4, ta tara wa kanta bashin Dalar Amurka biliyan 1.3 a cikin shekara…
Read More
Gwamna Sanwo-Olu ya sake buɗe kasuwar Mile 12 kwana biyu bayan rufe ta

Gwamna Sanwo-Olu ya sake buɗe kasuwar Mile 12 kwana biyu bayan rufe ta

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya bada umarnin gaggawa kan sake buɗe fitacciyar kasuwar nan ta Mile 12 biyo bayan gamsuwa da matakan tsaftace muhalli da aka ɗauka a kasuwar. A ranar Juma'ar da ta gabata gwamnatin jihar ta rufe kasuwar Mile 12 tare da kasuwar Owode Onirin saboda dalilai masu nasaba da rashin tsaftace muhalli. Sanarwar da gwamnatin ta fitar a ranar Litinin ta bakin Kwamishinan Muhalli da Ruwa na jihar, Mr Tokunbo Wahab, ta ce an sake buɗe kasuwar ce bayan gamsuwa da matakan tsaftace muhallin da aka ɗauka a kasuwar Kwsmishinan ya ce gwamnatin jihar ba ta…
Read More
Me ya biyo bayan rage farashin jakar sumunti da BUA ya yi zuwa Naira 3,500?

Me ya biyo bayan rage farashin jakar sumunti da BUA ya yi zuwa Naira 3,500?

Daga AMINA YUSUF ALI Rukunin kamfanoni na BUA ya ba da sanarwar rage farashin kamfani na sumunti i zuwa Naira 3,500 kowacce jaka. A halin yanzu dai ana sayar da shi a kan farashin kamfani na Naira 4,650, a kasuwa kuma ana sayar da shi Naira 5,000. A wani jawabi da kamfanin ya gudanar a ranar Lahadi, kamfanin ya sanar da cewa, sabon farashin zai fara aiki a ranar Litinin ɗin da ta gabata kamar yadda muka gani. Wani ɓangare na jawabin kamfanin mai taken, 'Ragi a farashin sumuntin BUA' ya bayyana cewa: “Kamar yadda muka faɗa a sanarwarmu ta…
Read More
Da sana’ar sayar da soson wanka mu ke samun rufin asiri a Ogun – Alhaji Ya’u

Da sana’ar sayar da soson wanka mu ke samun rufin asiri a Ogun – Alhaji Ya’u

Daga DAUDA USMAN a Legas Wani ɗan kasuwa mai gudanar da harkokin kasuwancin sayar da sosan wanka wanda ake kiransa da suna Kakan a Jihar Ogun, Alhaji Ya'u Samaila, ya bayyna cewa, da wannan sana'ar su ke samun rufin asiri a Ogun. Alhaji Ya'u, wanda ya kasance ɗan asalin ƙaramar hukumar Samaila ne da ke cikin Jihar Kano mazaunin Ogun, kuma shugaban Ƙungiyar Masu Sana'ar Kasuwancin Sosan Wanka Kakan a garin Ibafo ta Ogun ya bayyana cewa, shi da sauran 'yan Kasuwa masu sana'ar kasuwancin sosan kakan a garin Ibafo su na ƙara samun nasarori a wajen gudanar da harkokin…
Read More
Oyedele ga ‘yan Nijeriya – Gara ma ku yi fatan kar matatun mai su yi aiki a Nijeriya

Oyedele ga ‘yan Nijeriya – Gara ma ku yi fatan kar matatun mai su yi aiki a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Ɗaya daga cikin mataimakan da Shugaba Tinubu ya naɗa, Mista Taiwo Oyedele ya gaya wa 'yan Nijeriya cewa, su yi fatan kar Allah ya sa matatun man fetur su yi aiki a Nijeriya. Shugaban kwamitin shugaban ƙasa na tsare-tsaren kuɗi da saita haraji My MistaTaiwo Oyedele, shi ya isar da wannan gargaɗi ga 'yan Nijeriya. Ya ƙara da cewa, da zarar matatun sun fara aiki, litar man Nijeriya sai ta kere ta ko'ina a duniya tsada. Oyedele ya yi wannan jawabi ne a taron murnar ranar samun 'yancin kan Nijeriya da aka gudanar a ranar Litinin…
Read More
An sauke wa acaɓa, keke napep farashin fetur zuwa N430 a Borno

An sauke wa acaɓa, keke napep farashin fetur zuwa N430 a Borno

An sauke farashin litar mai zuwa Naira 430 don amfanin 'yan acaɓa da matuƙa adaidaita-sahu da 'yan taksi a jihar Borno. Bayanai sun ce ƙaddamar da dogayen motoci guda 70 da gwamnatin jihar ta yi don rage raɗaɗin rayuwa inda jama'a kan biya N50, hakan ya sa sauran masu abubuwa na 'yan kasuwa a jihar kowa na neman matsaya. An ce wasu masu hannu da shuni a jihar suka bai wa gidajen mai a babban birnin jihar kwangilar sayar da fetur N430 kan kowace lita a maimakon N637. Bayanai sun ce masu hannu da shunin sun ɗauki wannan mataki ne…
Read More
Rana ko iska a matsayin makamashi

Rana ko iska a matsayin makamashi

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Batunmu na wannan makon shine, hasken rana da kuma iska a matsayin sinadiran da za su samar da makamashi da zai samar da wutar lantarki ga gidajenmu da ofisoshinmu da guraren gudanar da sana’oi da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da kamfanoni da gonaki, kai da duk wuni guri da ake buƙatar wutar lantarki. Kimiya, wato Ilimin ƙwaƙwa da na ci da kuma zurfafa tunani kan al’amari mai tafiya da kuma komowa, sai kuma ilimin fasaha wato, ilimin sarrafa abubuwa zuwa wani abun. Ɗan Adam…
Read More
NNPCL ya yi wa wasu shugabannin kamfanin ma’aikatansa ritayar dole

NNPCL ya yi wa wasu shugabannin kamfanin ma’aikatansa ritayar dole

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin rarraba man fetur a Nijeriya (NNPCL) ya yi wa wasu daga cikin manyan ma'aikatansa/ shugabannin kamfanin ritayar dole. Wato ya tilasta wa wasu manyan ma'akatansa da wa'adin yin ritayar aikinsu ba ta wuce nan da watanni 15 masu zuwa ba yin ritayar dole. Wannan jawabin yana ƙunshe ne a cikin wani jawabi da hukumar gudanarwar ta kamfanin ta bayar a ranar Litinin ɗin da ta gabata ranar 18 ga Satumba, 2023, sannan ta wallafa a asusunta na shafin X (wanda da aka fi sani da Tiwita) a safiyar ranar Talata. Hakazalika, sanarwar ta bayyana cewa,…
Read More
‘Yan ƙasa ga Tinubu: Ba ma buqatar tallafin rage raɗaɗi, a rage mana farashin fetur kawai

‘Yan ƙasa ga Tinubu: Ba ma buqatar tallafin rage raɗaɗi, a rage mana farashin fetur kawai

*A zuba kuɗin tallafin rage raɗaɗi zuwa harkar ilimi da lafiya - 'yan ƙasa*Tallafin rage raɗaɗi ba shi da wata ma'ana - Inji ɗan kasuwa*Dole gwamnati ta sake tunani – Kwamared Alifia Daga AMINA YUSUF ALI A ƙoƙarinta na rage raɗaɗi da wahala da 'yan ƙasa suke sha a sakamakon cire tallafi a kan man fetur, gwamnatin tarayya ta shigo da tsarin ba da tallafin rage raɗaɗi, amma 'yan Nijeriya da suka samu kansu cikin matsuwa irin ta tattalin arziki sun fito sun bayyana cewa, sun fi qaunar a rage farashin man fetur fiye da tallafin rage raɗaɗin. Shugaba Bola…
Read More
UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), Mohamed bin Zayed Al Nahyan, sun cimma yarjejeniyar ɗage haramcin bai wa matafiya daga Nijeriya bisa ta shiga ƙasar. A ranar Litinin shugabannin biyu suka cimma wannan matsaya a Abu Dhabi, inda aka amince jiragen Etihad Airlines da na Emirates Airlines su ci gaba da zirga-zirga a Nijeriya nan take. Kuma yarjejeniyar ci gaba da zirga-zirgar jiragen ba ta shafi gwamnatin Nijeriya ta biya wasu kuɗaɗe nan take ba. La'akari da manufar Tinubu ta inganta tattalin arzikin Nijeriya haɗa da sauran tsare-tsaren bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da ya…
Read More