Kasuwanci

Minista Sadiya ta jajenta wa ‘yan kasuwar Guru da gobara ta yi wa ɓarna

Minista Sadiya ta jajenta wa ‘yan kasuwar Guru da gobara ta yi wa ɓarna

Daga AMINA YUSUF ALI Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Sadiya Farouq, ta bayyana jaje ga ‘yan kasuwar da gobara ta lashe wa dukiya a Babbar Kasuwar garin Guru a Jihar Yobe. Gobarar ta yi sanadiyyar ƙonewar sama da shaguna 300 tare da lalata dukiyar miliyoyin naira a ƙarshen makon da ya gabata. Hajiya Sadiya ta bayyana asarar da cewa babba ce, yayin da kuma ta umarci Hukumar Kai Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta gudanar da binciken gani-da-ido kan ibtila'in domin a san yawan asarar da aka yi. Ta ce, “Ina miƙa saƙon jaje ga gwamnatin Jihar…
Read More
Buhari ya zaɓi sabbin shugabannin hukumar kamfanin NNPC

Buhari ya zaɓi sabbin shugabannin hukumar kamfanin NNPC

Daga AMINA YUSUF ALI Shugaba Buhari ya zaɓi sababbin shugabannin hukumar kamfanin NNPC. Shugaban ƙasar Nijeriya, Muhammadu ya yi sabbin naɗe-naɗen muƙamai a sabon kamfanin NNPC. Shugaban ya yi wannan naɗi ne da amfani da damar ikon da sashe na 59(2) na sabuwar dokar man fetur a kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar (2021) ya ba shi. Kakakin Fadar Shugaban ƙasar, Mista Femi Adeshina shi ya tabbatar da wannnan labari ranar Larabar da ta wuce a Abuja. A cewar sa, an naɗa wasu muƙamai kamar haka: Shugabar Kwamitin ita ce Sanata Margret Chuba Okadigbo, sai Mele Kolo Kyari, a matsayin…
Read More
ECOWAS ta ba wa Najeriya mafita kan tafiyar hawainiya a sashen noma

ECOWAS ta ba wa Najeriya mafita kan tafiyar hawainiya a sashen noma

Daga AMINA YUSUF ALI Shugaban sashen harkar noma na gamayyar ƙungiyoyin Afirka ta Yamma (ECOWAS), Dakta Ernest Aubee ya yi kira ga Nijeriya da ta magance tafiyar hawainiyar da sashen noma yake yi a ƙasar. A cewar Ernest Aubee, wannan shi ne kaɗai abinda zai kawo mafita a kan matsalolin da suke kewaye da fataucin hatsin da ƙasar ta noma a tsakaninta da ƙasashen yankin na Afirka ta Yamma. Wasu daga cikin matsalolin da a cewar sa auke kawo cikas sun haɗa da, jinkirta motocin kayan abincin daga shiga bodar wasu ƙasashen, biyan maƙudan kuɗaɗen da ake yi kafin a…
Read More
An rufe kasuwanni a Jihar Oyo saboda rasuwar basarake

An rufe kasuwanni a Jihar Oyo saboda rasuwar basarake

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar litinin ɗin da ta gabata ne dai aka tashi da umarnin a rufe dukkan kasuwanni a jihar Oyo domin nuna girmamawa da alhini ga rasuwar Sarkin Ibadan ta jihar Oyo, (Olubadan); Oba Saliu Adetunji. Wannan umarni na rufe dukkan kasuwannin faɗin jihar ya fito ne daga babban shugaban kasuwanni na jihar ta Oyo, Asiwaju Yekini Abass wanda aka fi sani da YK Abass. Umarnin ya biyo bayan wani taron gaggawa na shugabannin kasuwanni na jihar da babban shugaban kasuwannin, YK Abass ya kira a ranar Lahadin da ta gabata. Wato jim kaɗan bayan mutuwar…
Read More
Kamfanin ExxonMobil ya jawo mana asarar biliyan 11 – Masuntan Akwa-ibom

Kamfanin ExxonMobil ya jawo mana asarar biliyan 11 – Masuntan Akwa-ibom

Daga AMINA YUSUF ALI Masunta a jihar Akwa-ibom sun koka a kan asarar Naira biliyan 11 da ta riske su. Inda suka ɗora zarginsu kacokam akan wani Ba'Amurken kamfanin komai da ruwanka na fetir da gas dake jihar. Inda suka ce ya yi buris da buƙatarsu da suka nemi ya biya su diyyar varin man fetur da kamfanin ya jawo. Wanda ya afku a tsakanin shekarar 1998 zuwa 2012. Masuntan sun bayyana cewa, bayan al'amarin ya faru, sun kai ƙara kotu. Amma ban-bakin da aka yi musu da fatan za a sulhuta a samu maslaha, ya sa suka janye ƙararsu…
Read More
Kamfanin lantarki da bankuna sun fi kowa shan ƙorafi a 2021 – Bincike

Kamfanin lantarki da bankuna sun fi kowa shan ƙorafi a 2021 – Bincike

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar kare haƙƙin masu saye  (FCCPC) ta bayyana cewa, Kamfanin wutar lantarki ya sake yin zarra a karo na biyu a matsayin kamfanin da ya fi kowanne amsar ƙorafi kamar dai yadda ya yi a shekarar bara ta 2020 ya sake yi a bana ma.  Kamfanin dillancin labarai (NAN) ya rawaito cewa, Shugaban zartarwa na  FCCPC, Mista Babatunde Irukerashi ne bayyana haka a ranar Lahadin da ta gabata a Abuja. Inda ya bayyana cewa, sashen banki shi ne ya biyo bayan kamfanonin lantarkin a matsayin na biyu wajen amsar ƙorafi.  Sannan su kuma kamfanonin zirga-zirgar jiragen…
Read More
Kaso 17.4% ne kawai na harajin 2021 ya shiga asusun Gwamnati – NNPC

Kaso 17.4% ne kawai na harajin 2021 ya shiga asusun Gwamnati – NNPC

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin Kula da man fetur, NNPC ya bayyana cewa, kaso 17.4 daga harajin da kamfanin ya tara a tsahon shekarar bara ne kawai ya shiga asususun kamfanin. Wato daga cikin kuɗaɗen da kamfanin ya tara Naira Tiriliyan 2.99, daga watan Janairu zuwa Nuwambar shekarar 2021.  A cewar NNPC, dukka ragowar kuɗaɗen an ɓatar da su ne a garin biyan kuɗin tallafin mai da laluben man fetur ɗin da kuma tafiyar da wasu al'amura a kamfanin. NNPC ta yi wannan bayani ne a cikin rahotonta ga kwamitin kula da asusun gwamnatin tarayya (FAAC) na watan Disamba wanda…
Read More
Ɗangote da BUA za su amfana da tallafin jarin sukari daga CBN

Ɗangote da BUA za su amfana da tallafin jarin sukari daga CBN

Daga AMINA YUSUF ALI Ana sa ran kamfanonin sukari na Ɗangote da BUA da sauran wasu kamfanonin sukarin za su amfana da jarin Dalar Amurka miliyan 73 a matsayin tallafin gwamnatin tarayya ga sashen samar da sukari a ƙasar.   Babban Bankin Nijeriya (CBN), da yawun gwamnatin tarayya, zai  ware Dalar Amurka Miliyan 73 domin ƙara bunƙasa harkar samar da sukari a ƙasar ta fuskar kayan aiki da injinan sarrafa sukarin da za su wadaci masana'antun sukari da suka kai faɗin hekta dubu goma.  Ministan masana'antu, Mista Niyi Adebayo, shi ya bayyana haka a Abuja ranar litinin ɗin da ta gabata.…
Read More
Gobarar shagon Next: Hukumar FEMA ta ƙaryata Pantami

Gobarar shagon Next: Hukumar FEMA ta ƙaryata Pantami

Daga AMINA YUSUF ALI Duk da yaɗuwar hotuna da bidiyo a shafukan yanar gizo da suke nuna cewa, mutane suna ta jidar kaya a yayin da wutar gobara take lamushe wani ɓangare na rukunin shagunan Next a Abuja, inda har ma daga bisani aka ga bidiyon Ministan Sadarwa, Sheikh Ali Isa Pantami, yana zubar da hawaye bisa takaicin yadda mutane suka riƙa satar kayayyaki a shagon, amma duk da haka Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Tarayyar Nijeriya (FEMA) ta ƙaryata wancan batu na cewa masu kwasar kayan nan da ake ta yaɗa hotunansu ɓarayi ne. Wannan batu dai ya…
Read More
Bankin Sterling zai fara gudanar da banki maras kuɗin ruwa

Bankin Sterling zai fara gudanar da banki maras kuɗin ruwa

Daga AMINA YUSUF ALI Bankin Sterling ya samu sahalewar Babban bankin Nijeriya, CBN a kan ya rikiɗewa ya koma kamfanin dillancin wasu kamfanonin. Kuma sannan ya buɗe sashen soma tafiyar da harkar banki mara kuɗin ruwa. Wanda ya laƙaba wa sunan, Alternative Bank Limited. A yanzu dai Bankin ya samu wannan lasisin daga CBN inda Babban Banki ya ba da lasisi a bisa wasu tsararrun dokoki da ya gindaya wa Bankin Sterling ɗin, kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito a ranar Larabar da ta gabata. Inda Bankin Sterling ya koma tsarin kamfanin dillancin wato 'holdco', hakan zai ba da…
Read More