21
Jun
Daga AISHA ASAS a Abuja biyo bayan tabbatar da jigo a jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓe mai zuwa, babban mawaƙin jam'iyyar, Dauda Kahutu Rarara, ya taya zaɓaɓɓen ɗan takarar murna tare kuma yin alƙawarin zai shirya tsaleliyar waƙa da zata shiga layin makaman yaƙin neman zaɓe. Rarara ya bayyana hakan ne a wata ziyarar taya murna da ya kai wa tsohon gwamnan Iko, shugaban jam'iyyar APC kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar, Bola Ahmed Tinubu. Babban mawaqin ya nuna jin daɗin sa kan nasarar da tsohon gwamnan ya samu…
