04
May
Daga BASHIR ISAH Gamayyar ƙungiyoyin masu shirya finai-finai a masana’antar Kannywood ƙarƙashin jagorancin MOPPAN da AFMAN sun aike wa Ministan Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed buɗaɗɗiyar wasiƙa suna masu sanar da shi dalilansu na ƙaurace wa bikin baje-kolin fina-fina da aka fi sani da ZUFF a taƙaice na 2022. Wasiƙar mai ɗauke da sa hannun Dr. Ahmad Muhammad Sarari na MOPPAN da Alhaji Sani Sule Katsina na AFMAN, ta nuna waɗanda lamarin ya shafa sun ƙi halartar bikin ne saboda nuna musu wariya da aka yi. Hukumar Kula da Harkokin Fina-finai na ta Ƙasa (NFC), ita ce mai shirya…
