Nishadi

Shakira ta amince da biyan Ƙasar Sifaniya tarar fam miliyan 6.5

Shakira ta amince da biyan Ƙasar Sifaniya tarar fam miliyan 6.5

Daga AISHA ASAS  Daga ƙarshe dai fitacciyar mawakiyar Colombia, Shakira ta cimma yarjejeniya da masu shigar da ƙara na Ƙasar Sifaniya kan sasantawa dangane da tuhumar almundahanar biyan haraji da ke kanta. Yarjejeniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin fara zaman kotu da ita. Mawakiyar ta biya tarar Yuro miliyan 7.5m, duk da cewa, a buƙatar masu gabatar da ƙara a yanzu sun so a ɗaure ta tsawon shekara takwas, sannan a ci ta tarar Yuro miliyan 23.8, idan aka same ta da laifi.  Kamar yadda Blueprint Manhaja ta ruwaito maku a 'yan watannin baya, mawaƙiyar ta…
Read More
An sallami wata jaruma daga fim bisa wallafa goyon bayan Falasɗinawa

An sallami wata jaruma daga fim bisa wallafa goyon bayan Falasɗinawa

Daga AISHA ASAS  Wata jaruma da ta ke aikin ɗaukar wani fim mai suna 'Scream' ta zama korarriya dalilin wallafa saƙon nuna goyon bayanta ga Ƙasar Falasɗinu, tare da barranta kanta daga irin kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza. Jarumar ta nuna matuƙar damuwa da halin da mutane ke ciki a Gaza, inda akai-akai ta ke wallafawa a shafukanta na sada zumunta ababen da ke wakana dangane da yaƙin Isra'ila a Gaza. A cikin irin rubutun nata, jarumar mai suna Melissa Barrera, ta zargi Isra’ila da aikata 'kisan ƙare dangi' wanda ke da ƙudurin shafe wata al'umma daga…
Read More
Rigima ta ɓarke tsakanin matar jarumi Mista Ibu da ‘yarsa kan kuɗin tallafi da ya samu

Rigima ta ɓarke tsakanin matar jarumi Mista Ibu da ‘yarsa kan kuɗin tallafi da ya samu

Daga AISHA ASAS A daidai lokacin da shahararren jarumi a masana'antar fim ta Kudu, wato Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da Mista Ibu ke kwance gadon jinya tare da alhinin iftila'in da ya saukar masa, its kuwa maiɗakinsa mai suna Stella Maris, da kuma 'yarsa ta riqo Jasmine Okafor, suka fara nuna wa juna yatsa danganen da kuɗaɗen da abokanen sana'arsa da masoyansa na faɗin duniya suka yi tururuwar tura masa, sa'ilin da aka nemi taimakon jama'a don sama masa lafiya. Kamar yadda sanannen shafi a kafar sada zumunta ta Instagram, Gistlover, ya wallafa hoton firar 'yar ta…
Read More
Yadda bikin auren jaruma Rashida Maisa’a ya gudana

Yadda bikin auren jaruma Rashida Maisa’a ya gudana

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano A ranar Asabar ɗin da ta gabata, 11 ga Nuwamba, 2023 ne aka ɗaura auren jaruma a Kannywood Rashida Adamu Abdullahi Maisa'a, da angonta Alhaji Aliyu Adamu, Sardaunan Matasan Gwoza. An ɗaura dai a layin Malam Bello a Unguwar Daurawa, daura da babban Titin Maiduguri a cikin garin Kano, kuma an samu halartar jama'a masu yawa da suka shaida an ɗaura auren. Ita dai Rashida Adamu Abdullahi ba ta shirya wani taron shagulgulan biki ba, kamar yadda jaruman fim suka saba yi. An dai tara malamai a gidanta inda suka wuni suna karatun Alƙur'ani mai…
Read More
Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Rasuwar Darakta Aminu Bono ta girgiza Gwamna Abba, cewar El-Mustapha

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna kaɗuwarsa bisa rasuwar fitaccen daraktan finafinan Hausa na Kannywood, Aminu S. Bono. Gwamna Abba ya bayyana hakan ne ta bakin Babban Sakataren Hukumar Tace Adabi na Jihar Kano, Abba El-Mustapha, wanda ya wakilce shi a wajen jana’aizar marigayin da aka gudanar ranar Talata, 21 ga Nuwamba, 2023, a maƙabartar Dandolo da ke birnin Kano. A ganawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala jana’izar, Abba ya kuma bayyana Marigayi Bono a matsayin mutumin ƙwarai mai haƙuri da yakana tare da kyakkyawar mu’amula, wanda kuma ya kai ƙololuwa wajen fikira…
Read More
Rasuwar Aminu Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje

Rasuwar Aminu Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje

Da BASHIR ISAH Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana rasuwar Darakta a Kannywood, Aminu Surajo Bono, a matsayin babban rashi ga masa'antar fina-finai. Ganduje ya bayyana kaduwarsa game da rasuwar marigayin, inda ya ce mutuwar tasa ta zo a daidai lokacin da aka fi bukatar marigayin. Sanarwar da Sakataren Yada Labarai ga Ganduje, Edwin Olofu, ya sanya wa hannu wadda aka kuma aka raba wa manema labarai a ranar Talata ta ce, “Bono ya yi wa takwarorinsa zarra wajen bada hima da kuma yada al'adun Hausa/Fulani”. Sanarwar ta kara da cewa, a halin rayuwarsa, marigayin…
Read More
Darakta a Kannywood, Aminu S. Bono ya riga mu gidan gaskiya

Darakta a Kannywood, Aminu S. Bono ya riga mu gidan gaskiya

Daga BASHIR ISAH Allah ya yi wa darakta a Kannywood, Aminu Surajo Bono, rasuwa a yammacin Litinin, 20 ga Nuwamba, 2023, bayan da ya yanke jiki ya faɗi. Da safiyar Talata, 21 ga Nuwamba, ake sa ran za a yi jana’izar marigayin a Kano. Wannan rashi ya kaɗa ‘yan fim su da sauran jama'a ainun, musamman ganin yadda rasuwar tasa ta yi ba-zata, ba ciwo ba ko hatsari. Marigayi Aminu yana daga cikin daraktocin da tauraronsu ke haskawa, musamman a ɓangaren bada umarnin shirya waƙa. Ya yi firamare da sakandire a Kano, sannan ya fara fim a shekarar 1999.
Read More
Mawaƙin Hausa ya nemi BBC ta biya shi diyyar miliyan N120

Mawaƙin Hausa ya nemi BBC ta biya shi diyyar miliyan N120

Daga AISHA ASAS  Wani mawaƙin Hausa da ya ke zaune a garin Kano, Abdul Kamal, ya ɗauki matakin shari’a kan tashar BBC Hausa bisa zargin amfani da sautin waƙarshi a shahararren shirin nan nasu da ke tattaunawa da jarumai da kuma mawaƙa mai suna ‘Daga Bakin Mai Ita’. Kamar yadda Barista Bashir Ibrahim Umar, lauya mai kare wanda ke ƙarar ya bayyana, amfani da BBC ta yi da sautin waƙar mawaƙi Abdul Kamal ba tare da izininsa ba koma baya ne ga cigabansa a harkar waƙa, domin mutane za su yi tunanin shi ne ya yi satar fasaha daga sautin…
Read More
Marubuci ne ke riƙe da fim bakiɗaya – Mubarak Dakta

Marubuci ne ke riƙe da fim bakiɗaya – Mubarak Dakta

"Sai an janyo marubuta jiki, an maIda su mutane ne za a ci moriyar harkar fim" Daga AISHA ASAS  A wannan sati, shafin Nishaɗi na Blueprint Manhaja ya karɓi baƙuncin wani haziƙin matashi, wanda ya samu shuhura a ɓangaren rubutun fim. Matashin, wanda ya ƙware ba a iya rubutun fim ba kaɗai, har ma da na zube, ya bayyana wa Bleprint Manhaja yadda ya fara da kuma finafinan da ya rubuta, kafin ya yi bayani kan muhimmancin marubuci a harkar fim da kuma irin yadda ake tauye marubuci a masana'antar finafinai. Idan kun shirya, Aisha Asas ce tare da Mubarak Idris…
Read More
Jarumi Samanja ya kwanta dama

Jarumi Samanja ya kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa jarumin wasan Hausa, Usman Baba Fategi da aka fi sani da Samanja, rasuwa. Majiyarmu ta ce, Samanja ya rasu ne da safiyar wannan Lahadin a wani asibitin Kaduna bayan fama da rashin lafiya. Duk da dai iyalan marigayin ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da rasuwar tasa, amma MANHAJA ta kalato cewa a wannan Lahadin za a yi jana'izar marigayin. Marigayin ya bar dunya yana da shekara 81, kuma ya rasu ya bar mata biyu da 'ya'ya 14. Samanja tsohon soja ne inda daga bisani ya kama aiki da Rediyon Tarayya…
Read More