Nishadi

Grammy Awards 2026: Daren da ya sanya duniya ta sake sanin ƙarfin waƙa

Grammy Awards 2026: Daren da ya sanya duniya ta sake sanin ƙarfin waƙa

Daga AISHA ASAS  A daren Lahadi, 1 ga Fabrairu, 2026, idanuwan duniya suka karkata zuwa birnin Los Angeles na ƙasar Amurka, inda aka gudanar da bikin karrama mawaka na Grammy Awards karo na 68 a babban dandalin Crypto.com Arena. Wannan taro, wanda ke ɗaya daga cikin manyan abubuwan nishaɗi a duniya, ya sake nuna matsayin sa a matsayin madubi da ke bayyana halin da duniyar waƙa ke ciki a kowace shekara. Rahotanni daga wajen taron sun bayyana cewa, dubban fitattun mawaƙa, masu shirya waƙoƙi, marubutan baitoci, da manyan jiga‑jigan masana’antar kiɗa sun halarci bikin, yayin da miliyoyin mutane a faɗin…
Read More
EFCC ta cika hannu da fitacciyar Jarumar Kannywood bisa zargin wulaƙanta Naira

EFCC ta cika hannu da fitacciyar Jarumar Kannywood bisa zargin wulaƙanta Naira

Daga AISHA ASAS  Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ƙasa (EFCC) ta kama fitacciyar jarumar Kannywood, Samha Inuwa, bisa zargin wulaƙanta kuɗin Najeriya, bayan bazuwar wani bidiyo da ke nuna tana amfani da takardun Naira wajen share majina daga hancinta. Bidiyon ya yaɗu cikin sauri a kafafen sada zumunta, inda jama’a suka rarrabu tsakanin masu kira da a hukunta ta da masu ganin a bi doka cikin natsuwa. Masana doka sun jaddada cewa, wulaƙanta Naira ba karamin laifi ba ne, kasancewar kuɗin ƙasa alama ce ta ’yancin kai da mutuncin ƙasa. EFCC ta bayyana cewa, wannan mataki na…
Read More
Gidauniyar Kannywood ta taya jaruma Aina’u Ade murnar naɗin da gwamnatin Kano ta yi mata

Gidauniyar Kannywood ta taya jaruma Aina’u Ade murnar naɗin da gwamnatin Kano ta yi mata

Daga AISHA ASAS  Gidauniyar Kannywood ta bayyana farin cikinta tare da taya Aina’u Ade murna bisa naɗin da Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi mata a matsayin Mai Ba da Shawara ta Musamman kan Harkokin Kannywood. A cikin wata sanarwa da Gidauniyar ta fitar, ta bayyana cewa nadin ya kasance ɗora ƙwarya a mazaunin ta, la’akari da shekaru na gogewa, ƙwazo da kuma manyan gudunmawar da Aina’u Ade ta bayar wajen bunƙasa da haɓaka masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood. Gidauniyar ta jaddada cewa Aina’a Ade ta kasance ɗaya daga cikin fitattun matan da suka yi…
Read More
Lamiyya: Nazarin waƙar  ‘La’ila’ ta Alhaji Auwal Umar Dangawuna

Lamiyya: Nazarin waƙar  ‘La’ila’ ta Alhaji Auwal Umar Dangawuna

Daga MD ASNANIC 1.0 Gabatarwa Bayyanannen abu ne cewa, mutanen da suka fara tsara waƙoƙi musamman domin yabon Annabi Muhammad (SAW) a duniya sun haɗa da: mahaifiyarsa Aminatu 'yar Wahabi da kakansa Abdulmuɗallib ɗan Hashim da mai rainonsa Halimatus Sa'adiya. Sai dai mutanen da suka fi shura a yabonsa bayan risala sun haɗa da Hassanu ɗan Sabitu da Ka'abu ɗan Zubairu da Abdullahi ɗan Rawaha. A ƙasar Hausa kuwa, mutanen da ake tunanin su suka fara tsara yabon Annabi (SAW) a waƙe tun a ƙarni na 13 zuwa na 17 sun haɗa da Wali ɗanmarina da Wali ɗanmasani da Abdullahi…
Read More
Tallafin Nuhu Ribadu: Yadda Musa Maisana’a ya raba abinci da kuɗi ga Jaruman Kannywood 

Tallafin Nuhu Ribadu: Yadda Musa Maisana’a ya raba abinci da kuɗi ga Jaruman Kannywood 

Daga MUKHTAR YAKUBU  Fitaccen jarumi a masana'antar Kannywood Musa Abdullahi, wanda aka fi sani da Musa Maisana'a, ya yi wani taro na rabon buhuhunan dhinkafa da kuɗaɗe ga wasu daga cikin jaruman Kannywood da suke cikin buƙatar taimako ta ɓangaren buƙatun rayuwar yau da kullum. Taron rabon kayan abinci da kuɗin wanda aka gudanar a ranar Litinin a cikin garin Kano ya samu halartar ɗimbin jama'a da suka halarci wajen domin samun rabon su na kuɗi da abinci da aka raba a wajen. A wajen taron dai an ga fuskokin tsofaffin jarumai masu yawa da suka halarci taron irin su…
Read More
Sharhin fim ɗin Balaraba

Sharhin fim ɗin Balaraba

Daga ABDULYASSAR AMINU ABUBAKAR Sunan fim: Balaraba Kamfani: Mai Shadda Global Resources Labari: Nura Hussaini Tsara Labari: Yakubu M. Kumo Daukar Hoto: Moses Stephen/Saifullahi Deen Sauti: Bello Minna Daukar Nauyi: Abubakar Bashir Mai Shadda Shiryawa: Abubakar Bashir Mai Shadda M/ Umarni: Sadik Sani Sadik Umarni: Abubakar Bashir Mai Shadda Fim ɗin Balaraba, wani fim ne da ya bayyana rayuwar wani matashi Umar Faruk,  mai tsananin fushi da hasala, ta yadda har ba ya iya yi wa harshensa linzami. Bai saurarawa kowa ba, abokai, dangi, kai har ma da mahaifinsa a wani takin. A tsaka da hakan ne auren shi ya…
Read More
Ku daina yin kuɗin goro kan harkar fim babu tarbiyya – Maryam Salisu

Ku daina yin kuɗin goro kan harkar fim babu tarbiyya – Maryam Salisu

Daga MUKHTAR YAKUBU  Sabuwar jaruma a masana'antar Kannywood Maryam Salisu ta fito shirin ta na zama babbar jarumar da kowa zai yi maraba da ita da zarar ta samu damar da za ta bajekolin basirar ta a cikin harkar ta Kannywood. Babu shakka idan har Maryam Salisu ta samu damar da take so ta samu na ɗaurin gindi daga masu juya harkar masana'antar, to ba abin mamaki ba ne cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ta kai ga matakin da kowa zai san da ita. Ba don komai ba kuwa sai don yadda Maryam Salisu ta kasance yarinya mai sauƙin kai da…
Read More
MOPPAN ta yi ta’aziyya bisa kisan uwa da ’ya’yanta shida a Kano

MOPPAN ta yi ta’aziyya bisa kisan uwa da ’ya’yanta shida a Kano

Daga AISHA ASAS  Haɗaɗɗiyar ƙungiyar Masu Shirya fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN) dake Arewa ta bayyana matuƙar alhini da jimami bisa mummunan kisan gillar da aka yi wa wata uwa da ’ya’yanta shida a unguwar Dorayi Chiranci da ke birnin Kano, lamarin da ya girgiza zukatan al’umma baki ɗaya. A wata sanarwar ta’aziyya da Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Shehu Hassan Kano, ya rattaba wa hannu, MOPPAN ta miƙa sakon jaje da tausayawa ga Gwamnatin Jihar Kano, ɗaukacin al’ummar jihar, da kuma iyalan mamatan, musamman Malam Haruna, mijin matar da aka kashe. Sanarwar ta bayyana cewa, wannan lamari na tayar da…
Read More
Fim ɗin ‘Kitso Da Kwarkwata’: Yadda sunansa ya bi shi tun farkon farawa

Fim ɗin ‘Kitso Da Kwarkwata’: Yadda sunansa ya bi shi tun farkon farawa

Daga MUKHTAR YAKUBU  A kwanakin baya kaɗan da suka gabata ne aka kammala ɗaukar wani sabon fim mai suna 'Kitso da Kwarkwata', wanda kamfanin shirya fina-finai mai suna Goldin Pin Multimedia ya ɗauki nauyin shiryawa. Mustapha Adam Muhammad shi ne ya zamo jagoran shirin, inda aka yi amfani da jarumai masu yawa – kama daga tsofaffin jarumai da kuma sababbi.  Fim ne mai dogon zango, wanda da zarar an kammala shi za a nuna shi a manyan gidajen talabijin da kuma manhajar YouTube da sauran manhajojin kallo. Kamar yadda binciken Blueprint Manhaja ya tabbatar ma na, farkon shirya fim ɗin…
Read More
Yadda fim ɗin ‘Behind The Scenes’ ya zama fim mafi kawo kuɗi a Nollywood

Yadda fim ɗin ‘Behind The Scenes’ ya zama fim mafi kawo kuɗi a Nollywood

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Fitacciyar jarumar finafinai kuma furodusa a Nollywood, Funke Akindele, ta kafa wani sabon tarihi a masana’antar shirya fina-finai a Afrika bayan da sabon fim ɗinta mai suna ‘Behind The Scenes’ ya zarce kuɗin shiga na Naira biliyan biyu a gidajen kallo. Rahotanni sun nuna cewa, fim ɗin ya zama na farko a tarihin Nollywood da ya taba kai wa wannan mataki a Afrika, lamarin da ya mayar da Funke Akindele babbar darakta kuma mai shirya fim mafi samun kuɗi a nahiyar baki ɗaya. A ranar Lahadi, 12 ga Janairu, 2025, Funke Akindele ta tabbatar da wannan…
Read More