Labarai

Zulum ya naɗa Indimi da wasu matsayin majalisar gudanarwa ta jami’ar Barno

Zulum ya naɗa Indimi da wasu matsayin majalisar gudanarwa ta jami’ar Barno

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnan jihar Barno, Babagana Umara Zulum, ya naɗa Majalisar Gudanarwa da za ta sanya ido kan gudanar da harkokin Jami'ar Jihar Barno. Zulum ya naɗa majalisar ne a ranar Litinin a fadar gwamnatin jihar, wadda za ta gudana ƙarƙashin jagorancin Alhaji Mohammed Indimi. Sauran mambobin majalisar sun haɗa da Farfesa Abubakar Mustapha, Farfesa Bankole Ogumbameru, Farfesa Shettima Umara Bulakarima, Alhaji Lawan Buba, wakilin majalisar dattawa na jami'ar da dai sauransu, yayin da rajistaran jami'ar zai kasance riƙe da muƙamin sakataren majalisar. Gwamnan ya yi kira ga 'yan majalisar da su samar da tsari mai inganci wajen…
Read More
Za a yi jana’izar mahaifiyar Sarkin Kano yau

Za a yi jana’izar mahaifiyar Sarkin Kano yau

Daga BASHIR ISAH Masarautar Kano ta bada sanarwar za a yi jana'izar mahaifiyar Sarkin Kano, marigayiya Hajiya Maryam (Mai Babban Ɗakin Kano), a yau Litinin. Masarautar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ta sami sa hannun Madakin Kano, Yusuf N. Ibrahim Chigari da aka fitar a jiya Lahadi. Sanarwar ta ce, "A bisa babban rashi da muka yi na rasuwar Mai Babban Ɗakin Kano, wanda ya faru Asabar 12 ga Ramadan 1442 (24 ga Afrilu, 2021)a ƙasar Masar, Masarautar Kano da Masarautar Bichi, na sanar da shirinjana'iza kamar haka: Ana tsammanin isowar mamaciya filin jirgin saman Malam Aminu…
Read More
An kama hanyar bai wa wasu marayu ilimi mai nagarta a Gombe

An kama hanyar bai wa wasu marayu ilimi mai nagarta a Gombe

Daga ABUBAKAR A. BOLARI, Gombe Shugaban gidauniyar zaka da waƙafi na jihar Gombe, Abdullahi Abubakar Lamiɗo, ya yi alƙawarin cewa gidauniyarsu da gidan Marayu na AL-GUH (Al- gidan Umma Hajara) za su haɗa kai dan ganin an bai wa marayu ilimi mai inganci dan su samu abun dogaro a rayuwa. Abudullahi Lamiɗo, ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar gidauniyar suka ziyarci gidan marayun a ranar Lahadi dan ba su tallafin kayan abinci cikin irin tsarin su na tallafa wa gajiyayyu da marayu a watan Ramadan. Ya koka kan irin yadda Musulunci yake da tsari ya kuma bayyana falalar…
Read More
Har yanzu ‘yan Boko Haram na riƙe da Geidam

Har yanzu ‘yan Boko Haram na riƙe da Geidam

Daga UMAR M. GOMBE Saɓanin bayanin da aka yi ta yaɗawa cewa an kashe mayaƙan Boko Haram tare da ƙwace garin Geidam daga hannunsu, wasu mazauna garin da suka buƙaci a sakaya sunansu sun tabbatar wa jaridar Neptune Prime lamarin ba haka yake ba. Sun ce har yanzu 'yan bindigar na riƙe da garin kuma sai ƙaruwar suke ta yi. Wani mazaunin garin da Neptune Prime ta samu zantawa da shi da sanyin safiyar Lahadi ya ce, "Na gan su da idanuna, waɗanda suka shigo shekaranjiya suna nan, sannan sun ƙaru daga daren da ya gabata zuwa wannan safiya." Wani…
Read More
Mutum 2 sun mutu a harin da aka kai gidan Gwamna Uzodinma a Imo

Mutum 2 sun mutu a harin da aka kai gidan Gwamna Uzodinma a Imo

Daga WAKILINMU Sahihan bayanai daga jihar Imo sun tabbatar da wasu mutum biyu sun rasa rayukansu yayin harin da 'yan bindiga suka kai wa gidan Gwamna Uzodinma da ke Omuma a yankin karamar hukumar Oru ta Yamma a jihar. Wannan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da gwamnan ya sanar da manema labarai cewa an yi nasarar kama wasu mutum 50 da ake zargi suna da hannu a hare-haren da aka kai a Imo lokacin bikin Easter da ya gabata, tare da cewa wasu 'yan siyasa ne suka ɗauki nauyinsu. Sai dai Manhaja ba ta samu tabbacin faruwar hakan ba…
Read More
Sojoji sun ragargaji ‘yan Boko Haram a Barno

Sojoji sun ragargaji ‘yan Boko Haram a Barno

Daga WAKILINMU Mayaƙan Boko Haram a Jihar Barno sun kwashi kashinsu a hannu bayan da Dakarun 'Operation Lafiya Dole' wanda a yanzu suke kan aiwatar da 'Operation Tura Takaibango' a yankunan Dikwa da Gulumba Gana, tare da haɗin gwiwar sojojin sama suka fatattake su Daraktan Hulɗa a Jama'a na sojojin, Brigadier General Mohammed Yerima shi ne ya bayyana haka. General Yerima ya ce 'yan ta'addan sun yi amfani da wasu motocin yaƙi ne wajen kai wa yankunan da lamarin ya shafa hari a Lahadin da ta gabata, kuma a daidai lokacin da jama'a ke shirye-shiryen buɗa bakin azumin wannan rana.…
Read More
Sufeto Janar ya bada umarnin janye manyan jami’an ‘yan sanda daga EFCC

Sufeto Janar ya bada umarnin janye manyan jami’an ‘yan sanda daga EFCC

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Riƙo na Rundunar 'Yan Sanda na Ƙasa, Usman Baba, ya bada umarnin janye manyan jami'an 'yan sanda da aka tura aiki a Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Umarnin na ƙunshe ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 15, Afrilu, 2021 wadda Usman Baba ya aike wa shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa. Wasiƙar wadda ta samu sa hannun Idowu Owohunwa babban jami'i na rundunar, ta nuna manyan jami'an 'yan sanda daga kan muƙamin CSP da aka tura aiki a EFCC, ana buƙatar su koma babban ofishin rundunar…
Read More
Gwamna Abiodun ya roƙi JUSUN ta janye yajin aikin da take yi

Gwamna Abiodun ya roƙi JUSUN ta janye yajin aikin da take yi

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, ya yi kira ga Ƙungiyar Ma'aikatan Fannin Shari'a ta Ƙasa (JUSUN) da ta duba sannan ta janye yajin aikin da ta tsunduma tun 6 ga Afrilu, 2021. Idan dai za a iya tunawa, mambobin JUSUN sun shiga yajin aikin gama gari ne domin neman a aiwatar da cin gashin kai ga fannin shari'a game da sarrafa kuɗaɗe kamar yadda kudin tsarin mulki ya amince da shi. Gwamnan ya yi wannan kira ne a lokacin da shugabannin JUSUN reshen jihar Ogun suka ziyarce shi a fadar gwamnatin jihar ƙarkashin jagorancin Mr Afolabi…
Read More
Mutum 164,488 aka tabbatar sun kamu da korona a Nijeriya -NCDC

Mutum 164,488 aka tabbatar sun kamu da korona a Nijeriya -NCDC

Daga AISHA ASAS Hukumar Yaƙi da Yaɗuwar Cututtuka ta Ƙasa (NCDC) ta bada sanarwar samun ƙarin mutum 65 da suka harbu da cutar korona cikin sa'o'i 24 a faɗin ƙasa. NCDC ta ce ƙarin da aka samu ya shafi wasu jihohi su 11 ne ciki har da jihar Lagos-41, Kaduna-6, Kano-3, Rivers-3, Plateau-3 da kuma Akwa Ibom-2. Sauran su ne; Imo-2 da Oyo-2 da Edo-1 da Bauchi-1 sai kuma jihar Osun mai mutum 1. A cewar NCDC, jimillar mutanen da aka tabbatar sun harbu da annobar a faɗin ƙasa ya kama 164,488, yayin da mutum154,441 sun warke, sannan mutum2,061 sun…
Read More
Jerin sunayen ɗalibai 17 da aka sace a jami’ar Greenfield

Jerin sunayen ɗalibai 17 da aka sace a jami’ar Greenfield

Daga AISHA ASAS An saki sunayen ɗalibai su 17 da aka yi garkuwa da su a Jami'ar Greenfield mai nisan kilomaita 34 da ke babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja. Wani ma'akacin jami'ar da ya buƙaci a sakaya sunansa, shi ne ya bayyana sunayen ɗaliban da lamarin ya shafa. Ma'akacin ya faɗa cewa ɗaya daga cikin masu gadin makarantar ya rasa ransa yayin harin wanda ya auku ranar Talata, 20 ga Afrilun 2021. Ga dai jerin sunayen ɗaliban da 'yan bindigar suka sace wanda baki ɗayansu maza ne babu mace ko guda: 1 Abraham Akinje 2 Fortune Alhassan 3 Miracle John…
Read More