01
May
Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yarda a biya masu karɓar fansho da sabon tsarin albashi mafi ƙaranci. Sakatariyar Hukumar Fansho, Dr Chioma Ejikeme, ita ce ta bayyana haka yayin taron manema labarai a Abuja a Juma'ar da ta gabata. Jami'ar ta ce da wannan amincewar da aka samu daga wajen Shugaban Ƙasa, an ƙarfafa wa kwamitin PTAD kan ya soma gyare-gyare game da abin da ake biyan masu karɓar fansho domin ya daidaita da sabon tsarin biyan haƙƙoƙin nasu. Ejikeme ta ce sabon tsarin biyan fansho ɗin zai soma aiki ne daga Mayu, 2021. Ta kara da…
