18
Feb
*Gwamnoni za su yi ’yan sandansu*Ya umarci shugabannin tsaro su dirar wa masu ɓoye abinci Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A jiya Alhamis ne Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, tare da gwamnoni suka amince da kafa ’yan sandan jihohi a ƙasar. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Ƙasa, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa a ƙarshen wani taron gaggawa da shugaban ya kira a zauren majalisar da ke Fadar Shugaban Qasa a Abuja. Ministan ya ce, za a gudanar da tarurruka da dama,…
