Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayya ta bakin Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Isa Pantami, ta bayyana cewa an samu jimillar hare-hare 12,988,978 da suka samo asali daga ciki da wajen Nijeriya a lokacin zaɓen Shugaban Ƙasa da ya gudana 25 ga Fabrairu, 2023. A cewar Pantami, a kullum ana samun barazanar da bai gaza 1,550,000 ta yanar gizo da kafofin sadarwa, inda ya ƙara da cewa alƙaluma daga bisani suka haura zuwa 6,997,277 a ranar zaɓen Shugaban Ƙasa. Wata sanarwa a ranar Talata ta bakin mai magana da yawun Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na…