06
Mar
*An kama waɗanda ake zargi Daga BASHIR ISAH Aƙalla 'yan banga 10 ne aka tsare bisa zargin kisan malamin addini a Jihar Zamfara. MANHAJA ta rawaito an kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ne a ranar Talata a garin Mada da ke cikin yankin Ƙaramar Hukumar Gusau a jihar. Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya ce waɗanda hukuma ta kama 'yan banga ne ba jami'an bai wa al'umma kariya (CPG) ba. MANHAJA ta rawaito ana zargin jami'an CPG da yi wa Sheikh Abubakar Hassan Mada kisan gilla, lamarin da ya jefa al'ummar jihar cikin ruɗani. Sai dai sanarwar da Sulaiman…
