Babban Labari

Ba jami’an CPG suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ba – Gwamnatin Zamfara

Ba jami’an CPG suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ba – Gwamnatin Zamfara

*An kama waɗanda ake zargi Daga BASHIR ISAH Aƙalla 'yan banga 10 ne aka tsare bisa zargin kisan malamin addini a Jihar Zamfara. MANHAJA ta rawaito an kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ne a ranar Talata a garin Mada da ke cikin yankin Ƙaramar Hukumar Gusau a jihar. Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya ce waɗanda hukuma ta kama 'yan banga ne ba jami'an bai wa al'umma kariya (CPG) ba. MANHAJA ta rawaito ana zargin jami'an CPG da yi wa Sheikh Abubakar Hassan Mada kisan gilla, lamarin da ya jefa al'ummar jihar cikin ruɗani. Sai dai sanarwar da Sulaiman…
Read More
Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Daga BASHIR ISAH Matamakin shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya bayyana cewa abin da aka shuka a baya shi ake girba a yanzu dangane da tsadar rayuwar da ake fuskanta a ƙasa. Shettima ya buƙaci ‘yan Nijeriya da a kula da yadda suke bayyana fushinsu game da matsalolin tattalin arzikin da ƙasa ke fama da su a wannan hali. Ya ce dukkanin abubuwan da ake gani a yanzu sakamakon abubuwan da aka aikata a gwamnatocin a baya ne wanda ƙasar ke ƙoƙarin daidaita komai don inganta tattalin arzikin ƙasa. Ya ci gaba da cewa, kamar kowace gwamnati, ita gwamnatin Shugaba Bola…
Read More
Tinubu ga ’yan Nijeriya: Wahalarku ba za ta tashi a banza ba

Tinubu ga ’yan Nijeriya: Wahalarku ba za ta tashi a banza ba

*Shugaban ya ɗora alhakin taɓarɓarewar tattalin arziki a kansa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɗauki cikakken alhakin taɓarɓarewar tattalin arzikin da 'yan Nijeriya ke fuskanta tare da tabbatar wa 'yan ƙasar cewa, wahalhalun da suke fama da shi ba zai faɗi wasa banza ba. Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga shugabannin ƙungiyar Afenifere a gidan Pa Reuben Fasoranti da ke Akure, Jihar Ondo, a ranar Laraba, 28 ga Fabrairu, 2024. A cewar wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya fitar, shugaban…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Shugaban Hisbah, Sheikh Daurawa ya ajiye muƙaminsa

Da Ɗumi-ɗumi: Shugaban Hisbah, Sheikh Daurawa ya ajiye muƙaminsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Hisbah a Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya sanar da ajiye muƙaminsa a matsayin Babban Kwamandan Hisbah, tare da nuni davrashin ƙwarin gwiwa daga ɓangaren Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. Daurawa ya ce duk da ƙoƙarin da yake yi wajen kyauta tarbiyya a jihar a matsayinsa na shugaban Husbah, amma cewa ya karaya da yanayin kamalaman gwamnan. Faifan bidiyonnya ya yaɗa a shafinsa na soshiyal midiya, Malamin ya ce, "Yanzu haka ina Jihar Kaduna ina ganawa da 'yan majalisa ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar don tattauna aiwatar da dokar yin gwaji kafin aure a Kano…
Read More
Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa

Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar mata ta neman tsige Mataimakin Babban Jami'in Hukumar FCCPC, Barrister Babatunde Irukera. Wasiƙar da Tinubun ya aike wa Majalisar wadda Shugaban Majalisar ya karanto ta yayin zaman Majalisar a ranar Laraba, ta nuna Tinubu ya buƙaci tsige Irukera ne saboda rashin kataɓus. Dokar FCCPC ta tanadi cewa, sai da sahalewar Majalisar Dattawa kafin Shugaban Ƙasa zai iya tsige Mataimakin Babban Jami'in Hukumar. Sanarwar da ta nuna tsige Irukera ta sake nuni da yadda Tinubu ya tsige Babban Daraktan hukumar Bureau of Public Enterprises (BPE), Alex…
Read More
Sake fasalin hukumomin gwamnati: Tinubu ya bada umarnin ɗabbaƙa Rahoton Oronsanye

Sake fasalin hukumomin gwamnati: Tinubu ya bada umarnin ɗabbaƙa Rahoton Oronsanye

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya bada umarnin gaggawa jan ɗabbaƙa rahoton Kwamitin Shugaban Ƙasa Kan Sake Fasalin Hukumomin Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ma'aikatan Tarayya, Mr Stephen Osagiede Oronsaye. Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Mohammed Idris ya sanar da manema labarai hakan jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zatarwa (FEC) a Abuja a ranar Litinin. Idris ya ce matakin zai shafi ma'aikatu da dama inda za a shafe wasu, sannan a gwamasu da wasu daidai da shawarwarin da kwamitin ya bayar. Ya ce, “A yau Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki muhimmin…
Read More
‘Yunwa ta sa kan ‘yan Nijeriya ya haɗu’ – Obi

‘Yunwa ta sa kan ‘yan Nijeriya ya haɗu’ – Obi

*Ya cacaki gwamnatin Tinubu Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ƙalubalanci gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan tsadar kayan abincin da ake fama da ita a ƙasa, yana mai cewa a halin da ake ciki "yunwa ta haɗa kan 'yan ƙasa." Obi ya bayyana haka ne a ranar Litinin, inda ya ce gwamnati ta gaza daƙile matsalar hauhawar farashin kayan abincin da ke ci gaba da addabar 'yan ƙasa. A cewarsa, “A yau, mun zama ƙasa wadda yunwa ta haɗe kanta lamarin da ya kai wasu na mutuwa saboda yunwa da wahala. "'Yan…
Read More
Wata biyar ana garkuwa da ’yan matan Zamfara

Wata biyar ana garkuwa da ’yan matan Zamfara

*’Yan bindiga sun nemi a saki babansu, cewar iyayen yaran*Ba ni da masaniya, inji Gwamnan Dauda Daga SUNUSI MUHAMMAD a Gusau A halin da ake ciki yanzu kimanin watanni biyar da suka gabata kenan da wasu ’yan ta’adda suka afka wa gidajen kwanan ɗaliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da kimanin ɗalibai mata 30 da wasu ma’aikatan kamfanin gine-gine su tara yayin da a halin yanzu kimanin ɗalibai mata 12 suka rage har yanzu babu wani cikakken bayanin akansu. Wakilin Blueprint Manhaja a Zamfara, SANUSI MUHAMMAD, ya yi bincike game…
Read More
ECOWAS ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa Nijar, Burkina Faso, Mali, Guinea

ECOWAS ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa Nijar, Burkina Faso, Mali, Guinea

ECOWAS ta yanke shawarar ɗage wasu takunkuman da ta ƙaƙaba wa ƙasashen Jamhuriyar Nijar da Mali da Guinea. Ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a wajen taronta da ta shirya ranar Asabar a Abuja. Sai dai ɗage takunkumin ba na baki ɗaya ba ne, wasu ne daga cikin takunkuman da ECOWAS ɗin ta kafa wa ƙasashen da lamarin ya shafa. Idan ba a manta ba, a watan Janairun da ya gabata Nijar da Mali da Burkina Faso suka sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ECOWAS sakamakon takunkuman da aka kafa musu biyo bayan juyin mulkin da ya faru a ƙsashen.
Read More
Za a yanke wutar lantarki a Fadar Shugaban Ƙasa da CBN saboda bashi

Za a yanke wutar lantarki a Fadar Shugaban Ƙasa da CBN saboda bashi

Daga BASHIR ISAH Kamfanin rarraba wutar lantarki, wato Abuja Electricity Distribution Company, ya ba da sanarwar zai yanke wutar lantarki a Fadar Shugaban Ƙasa da Babban Bankin Nijeriya (CBN) da wasu ma'aikatu da hukumomi 85 na Gwamnatin Tarayya saboda bashin kuɗin wuta da ya kai sama da Naira biliyan 47,195 ya zuwa Disamban 2023. AEDC ya bayyana haka ne a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, 19 ga Fabrairu, 2024. AEDC ya bayyana cewa, “Hukumar Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) ta bada wa'adin kwana 10 ga ma'aikatu da hukumomin gwamnati 86 kan su biya bashin kauɗin wuta, N47.1bn…
Read More