Adabi

Kasuwancin littattafai a onlayin babban cigaba ne – Zulaihat Rano

Kasuwancin littattafai a onlayin babban cigaba ne – Zulaihat Rano

"Ta bincike da tunasarwar manyan marubuta nake samun hikimar rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Daga cikin marubutan Hausa da suka ci kasuwar littattafai tun zamanin adabin kasuwar Kano ke tashe, kuma yanzu suka dawo suka rungumi tsarin rubutun onlayin, akwai marubuciya Zulaihat Haruna Rano, daga Jihar Kaduna, wacce ta yi rubuce-rubuce da dama, masu ilimantarwa da nishaɗantarwa. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, ya tattauna da ita game da inda ta sa alqiblar rubutunta da kuma hasashenta kan cigaban harkar rubutun adabi, musamman yanzu da abubuwa suke komawa yanar gizo. Ga yadda hirar ta su ta kasance.…
Read More
Adamu Ɗan Maraya Jos

Adamu Ɗan Maraya Jos

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan Maraya Jos (an haife shi Adamu Wayya, 20 Disamba 1946 – 20 Yuni 2015) fitaccen mawaƙin Hausa ne daga Jos, Nijeriya. Ya shahara da salon waƙoƙinsa na musamman wanda ya haɗa waƙoƙin Hausa da jigogi da kayan kiɗa na zamani. An haifi Ɗan Maraya Jos a Sabon Gari, al’ummar Hausawa da suka fi yawa a garin Jos na Jihar Filato a Nijeriya. Ya girma a cikin gida na kiɗa kuma ya fara yin wasa tun yana ƙarami. Kakansa ne ya zaburar da shi, wanda ya kasance mawaƙin gargajiya na Hausa, ya kuma koyi yin kiɗa…
Read More
Sheikh Dakta Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya)

Sheikh Dakta Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya)

An haife shi a cikin garin Gaya ta Jihar Kano a shekarar 1950. Ya haddace Alƙur'ani ya na da shekara 11, ya gama duk wani fanni na ilimi da ake karantawa a makarantun soro (ƙarshen ilimi kenan a wancan lokacin) yana da shekaru 15. Ya fara rubutun Alkur'ani yana da shekaru 13, ya zama Alaramma mai darasu tun ina da shekaru 14.Tsangayar sa tana nan a halin yanzu a Gashua, a Katuzu/Garin Yamma, jihar Yobe. Malam Musa Dan Dikkware shi ne Halifa sa mai darasu a halin yanzu. Ya fara shimfiɗa buzu na karantar da ɗalibai a makarantar soro tun…
Read More
Tarihin Marigayi Yusuf Maitama Sule, Ɗan Masanin Kano

Tarihin Marigayi Yusuf Maitama Sule, Ɗan Masanin Kano

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sanin mutum sai Allah! Daga cikin mutane, akwai waɗanda Allah ke yi wa baiwar da bayyana ta ke da matuƙar wahala. Irin waɗannan mutane, rayuwarsu cike ta ke da darrusan da za a iya koya. Alhaji Yusuf Maitama Sule, Ɗanmasanin Kano, ɗaya ne daga cikin irin waɗannan mutane. Mutum ne mai ilimin addini da kuma na zamani. Allah ya yi masa baiwa da haƙuri, gaskiya, riƙon amana, cika alƙawari, sada zumunci, yafiya, barkwanci, dogaro da kai, da kuma sadaukar da kai. Mutum ne ɗan kishin ƙasa, mai son ganin jama’a sun ci gaba, mai son zaman…
Read More
Marigayi Sarkin Kano Muhammadu Rumfa

Marigayi Sarkin Kano Muhammadu Rumfa

Daga SADIQ TUKUR GWARZO Cikakken sunan sa shi ne Muhammadu Rumfa ɗan Yaƙubi, sunan mahaifiyarsa Faɗimatu, ance ita mutuniyar ƙasar Rano ce. Muhammadu Rumfa nagartaccen mutum ne, adali, malami, wanda ba za a samu wani tamkarsa ba a cikin sha'anin mulkin Kano. Akwai zantuka game da yadda aka sanya masa suna RUMFA. Zance na farko na cewa saboda a saman Rumfa ake ajiye masa abinci sa'ar da ya zama sarki wai saboda dabbobi na zagayawa su lalata kafin ya baro fada. Na biyu kuma mafi inganci shine bisa kasancewarsa Rumfa majinginar 'yanuwansa da sauran al'umma, watau mai taimako da shiga…
Read More
Sharhin littafin ‘GAWA da RAI’

Sharhin littafin ‘GAWA da RAI’

Daga BAMAI A. DABUWA KKM Sunan Littafi: Gawa da Rai.Sunan Marubuci: Yusuf Yahaya Gumel.Shekarar Bugu: 2022.ISBN: Babu.Bugu: AGK Graphics Kurna.Yanayi: Ba A Fayyace ba.Jigo: Soyayya.Salo: Cikin Fage.Mai Sharhi: Bamai A. Dabuwa Kkm.Lambar Wayar Mai Sharhi: 07037852514.Email: [email protected] GABATARWA/TSOKACI. Littafin Gawa da Rai, labari ne na wani matashi (Anas), mai fama da larurar 'Cotard Delusion'. Wata kalar cuta ce, da idan ta kama mutum sai kawai ya gamsu a ransa cewa shi matacce ne ko kuma dai ya rasa wani sashe na jikinsa, alhalin ba hakan ba ne. Tauraron ya kamu da soyayyar wata yarinya (Laila). 'Yar gidan wani hamshaƙin mai…
Read More
Marigayi Mamman Shata: Shekaru shekaru 24 da rasuwarsa

Marigayi Mamman Shata: Shekaru shekaru 24 da rasuwarsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A rana mai kamar ta yau (18 ga watan Yuni 1999) Allah Ya yi wa shahararren mawaqin Hausa Dr. Mamman Shata Katsina Rasuwa. Bayani Kaɗan A Kan Shata: An dai haifi Marigayi Alhaji Dr. Mamman shata a garin Musawa, A Shekarar 1923, kuma ya girma a katsina wato Jihar Katsinan Tarayyar Nijeriya. Ya yi ƙaura zuwa garin kano ya kuma rasu a ranar 18 Yunin Shekarar 1999 an binne shi a garin Daura kamar yadda yabar wasiya, To a lokacin da Marigayi Dr. Mamman Shata ya ke a raye akwai tambayoyi makamanta waxanda Malam Ɗan’zumi ya…
Read More
A baya akasarin manyan marubuta suna hantarar ƙanana masu tasowa – Gimbiya Amrah

A baya akasarin manyan marubuta suna hantarar ƙanana masu tasowa – Gimbiya Amrah

"Marubutan littafi da na onlayin gudunmawa ɗaya suke bayarwa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Gimbiya Amrah Auwal Mashi, fitacciyar marubuciyar online ce daga Jihar Katsina. Tana daga cikin matasan marubutan da suka ciri tuta, a fannin rubuce-rubucen almara da jarumta. Tun da ta rungumi alƙalami a shekarar 2014 har yau ba ta ajiye ba. Rubutu take yi babu kama hannun yaro, a ƙalla yanzu tana da littattafan da ta rubuta sun fi 20. A zantawarta da wakilin Manhaja Blueprint, Gimbiyar ta bayyana irin nasarorin da ta riqa samu a gasanni daban-daban, ciki har da Gasar Hikayata, Mu Gani A Ƙasa, da…
Read More
Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dangane da adabin Hausa da adabin Arewacin Nijeriya, Alhaji Abubakar Imam na ɗaya daga cikin manyan marubutan da rubuce-rubucensu suka yi nuni da al’adun Arewa. Sai dai ba abun mamaki ba ne yadda ya fito daga jihar Neja, wadda daman jiha ce mai daɗaɗɗen tarihi na marubuta masu hazaƙa. Ya rubuta litattafai da dama da suka rayu har bayan rasuwarsa. Don fahimtarsa, mutum na buƙatar karanta ko wane shafi masu ban sha'awa na littattafansa don gane wa kansa wane ne Alhaji Abubakar Imam. Malami ne, mai kishin ganin al'ummarsa sun sami ilimi. Har ila yau, ya…
Read More
Samun haɗin kan marubuta ne babban burina – Rufaida Umar

Samun haɗin kan marubuta ne babban burina – Rufaida Umar

"Addu'a ce sirrin samun nasarata a gasar rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kamar yadda rayuwa take nuna kowa da rabonsa a duniya, kuma kowa da irin tanadin da ubangiji ya yi masa. Haka yake kasancewa a rayuwar marubuta, kowa da yadda harkokin rubutunsa ke tafiya. Wani cikin sauri da samun nasara akai akai, wani kuma sai ya yi aiki tuƙuru kafin ya cimma nasarar da yake nema. Rufaida Umar Ibrahim na ɗaya daga cikin irin waxannan marubuta da za a iya kira da ƴan baiwa, saboda yadda suke samun nasarori cikin rubuce-rubucensu, musamman ma dai a gasar rubutun Gajeren Labari…
Read More