Siyasa

PDP za ta gudanar da babban taronta a Oktoba – Tambuwal

PDP za ta gudanar da babban taronta a Oktoba – Tambuwal

Jam'iyyar PDP ta ba da sanarwar cewar za ta gudanar da babban taronta na ƙasa tsakanin ranar 30-31 ga Oktoba mai zuwa idan Allah Ya kai mu. Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP, Aminu Tambuwal ne ya shaida wa manema labarai hakan jim kaɗan bayan kammala wani taronsu a Abuja a jiya Juma'a. Tambuwal ya ce za su miƙa shawarwarinsu dangane da taron ga shugabancin jam'iyyar na ƙasa, tare da cewa shugabannin ne za su tsayar da inda taron zai gudana. Kazalika, Tambuwal ya ce sun haɗa wata tawaga ta mutum takwas ƙarƙashin jagorancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Marka, da…
Read More
Harin ta’addanci ya laƙume rayuka 11 a Kabul

Harin ta’addanci ya laƙume rayuka 11 a Kabul

Fashewar wani abu mai ƙarfi da ya auku ran Alhamis ya yi sanadiyar mutuwar mutum 11 a tashar jiragen saman Kabul da ke Afghanistan. Wannan na zuwa ne 'yan sa'o'i bayan da ƙasashen yammacin duniya suka yi gargaɗin yiwuwar samun harin ta’addanci a filin jirgin da ke ɗauke da dubban mutanen da ke ƙoƙarin ficewa daga ƙasar. Mai magana da yawun ma’aikatar tsaron Amurka, John Kirby, ya tabbatar da aukuwar fashewar, sai dai ya zuwa haɗa wannan labari ba a kai ga tantance irin irin ɓarnar da ta aukuwa ba sakamakon fashewar. Amma wani jami’in ƙungiyar Taliban ya ce mutanen…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: An tsige Shugaban Majalisar Kebbi da mataimakinsa

Da Ɗumi-ɗuminsa: An tsige Shugaban Majalisar Kebbi da mataimakinsa

Rahotannin da MANHAJA ta samu daga jihar Kebbi na nuni da cewa, 'yan Majalisar Dokokin jihar sun tsige Shugaban Majalisar, Samaila Abdulmunin Kamba da mataimakinsa, Muhammad Buhari Aleiro daga muƙamansu. Binciken MANHAJA ya gano cewa, mambobi 20 daga cikin 'yan majalisa 24 da Majalisar Jihar ke da su ne, suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan tsige waɗanda lamarin ya shafa a wannan Talatar. Bayan tsigewar, ba tare da ɓata lokaci ba 'yan majalisar suka zaɓi Mohammed Abubakar Lolo da Muhammad Usman Ankwai a matsayin sabbin shugabannin majalisar. Duk da dai babu wani cikakken bayani kan dalilin da ya sa aka tsige tsoffin…
Read More
Rashin tsaro: INEC ta tsaida aikin rajistar zaɓe a ƙananan hukumomi 5 a Filato

Rashin tsaro: INEC ta tsaida aikin rajistar zaɓe a ƙananan hukumomi 5 a Filato

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta dakatar da aikin rajistar masu zaɓe da ake yi a faɗin ƙasar nan a ƙananan hukumomi biyar na Jihar Filato. A wata sanarwa da Madam Caroline Okpe, Sakataren Gudanarwa ta INEC, ta fitar a madadin Kwamishinan Zaɓe mai zama a jihar (REC), a ranar Litinin a Jos, ta ce an ɗage aikin ne saboda dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta saka. Ta ce, “Ɗage aikin zai shafi cibiyoyin rajistar a ƙananan hukumomin Barkin Ladi, Bassa, Jos ta Gabas, Jos ta Arewa da kuma Riyom har sai hali ya yi. “INEC ta na tabbatar wa da sababbin…
Read More
Buni ya jagoranci gwamnonin APC don zawarcin Rashidi Ladoja a Ibadan

Buni ya jagoranci gwamnonin APC don zawarcin Rashidi Ladoja a Ibadan

Daga AMINA YUSUF ALI A Lahadin da ta gabata gwamnonin APC guda uku suka ziyarci Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, domin zawarcin dattijon jam'iiyyar PDP kuma tsohon gwamna, Alhaji Rashidi Ladoja, zuwa jam'iyya mai mulkin ƙasa ta APC. Gwamnonin sun yi wannan tafiya ne a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kwamitin Riƙo na jam'iyyar APC, Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe. Har ila yau, Gwamnonin sun ziyarci wani babban mutum na Majalisar Dattijan Yarbawa, (YCE), Dakta Kunle Olajide. Sai kuma sarkin Musulmi na Ƙasar Yarabawa, Alhaji Dawud Akintola. A tare da Mai Mala Buni akwai Gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu da…
Read More
Na yi tsufa da takarar sanata a 2023 – Masari

Na yi tsufa da takarar sanata a 2023 – Masari

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamna Aminu Bello Masari na Jahar Katsina ya ƙaryata zargin cewa yana hararar wata kujerar mulkin bayan kammala wa'adin zangon mulkinsa na biyu a shekarar 2023. Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen wani taro inda ya bayyana cewa, ya riga ya yi wa mutane hidima da dama a ɓangarori daban-daban a tsawon rayuwarsa. Don haka yanzu ba zai sake neman wani muƙamin ba sai dai ya tallafi matasa 'yan baya su samu muƙamai a gwamnati. Amma sam shi ba zai ƙara neman muƙami ba, walau na gwamnati ko kuma na jam'iyya. Ya ƙara da cewa,…
Read More
2023: Masu shirin tafka maguɗi ku fice daga Binuwai ko ku kuka da kanku – Gwamna Ortom

2023: Masu shirin tafka maguɗi ku fice daga Binuwai ko ku kuka da kanku – Gwamna Ortom

Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai ya yi gargaɗin cewa masu shirin tafka maguɗin zabe a 2023, mafi alheri a gare su shi ne su fice daga jihar ko kuma su kuka da kansu. Ortom ya yi wannan gargaɗi ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a Makurɗi bayan da ya dawo daga taronsu na Ƙungiyar Gwamnonin PDP da suka gudanar a Abuja. A cewar gwmnan, "Ina tuanin cewa a matsayinmu na ƙasa mun samu cigaba, bai kamata mu koma rayuwa irin ta da ba alhalin duniya baki ɗaya ta bunƙasa." Ya ci gaba da cewa wajibi ne Shugaban Ƙasa…
Read More
INEC ta fitar da jadawalin ranakun rajistar masu zaɓe

INEC ta fitar da jadawalin ranakun rajistar masu zaɓe

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana ranaku da abubuwan da za a yi dangane da rajistar masu jefa ƙuri'a da ake gudanarwa a yanzu. Idan kun tuna, an fara aikin ne daga ranar 28 ga Yuni, 2021 kuma za a ci gaba da yin sa har zuwa ranar 11 ga Yuli, 2022. A sanarwar da sashen yaɗa labarai da wayar da kan masu zaɓe na hukumar ya fitar, an nuna cewa za a yi aikin a watanni uku na farko da watanni uku na biyu na wannan shekarar da mu ke ciki. A baɗi kuma za a…
Read More
Gazawa ce idan APC ta jajubo Jonathan a 2023 – Hon. Tasiu Danhajiya

Gazawa ce idan APC ta jajubo Jonathan a 2023 – Hon. Tasiu Danhajiya

Daga NASIR S. GWANGWAZO An bayyana cewa, ba ƙaramar gazawa ba ce ga jam’iyyar APC mai mulkin Nijeriya matuƙar ta yi kuskuren bai wa tsohon Shugaban Nijeriya, Dr. Goodluck Ebele Jonathan, takara a lokacin Babban Zaɓen shekara ta 2023 da ke tafe. Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Hon. Tasiu Sani Danhajiya, Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kano da Kewaye kuma ɗan jam’iyyar APC. Idan dai za a iya tunawa, rahotanni na nuni da cewa, akwai wani tsari a ƙarƙashin ƙasa da ake yi tsakanin wasu jiga-jigan APC daga Arewacin Nijeriya na dawowar Mista Jonathan cikin…
Read More
Za mu iya tattara sakamakon zaɓe ta amfani da fasahar zamani – INEC

Za mu iya tattara sakamakon zaɓe ta amfani da fasahar zamani – INEC

Daga WAKILINMU Duk da ra'ayin da wasu 'yan majalisun tarayya suka yi kan cewa batun tattara sakamakon zaɓe ta hanyar amfani da fasahar zamani abu ne da ba zai yiwu ba saboda rashin hali ta ɓangaren Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) da kuma rashin wadatar netiwoki a wasu sassan ƙasa, sai ga shi Asabar da ta gabata aka ji INCE ɗin ta fito ta bayyana cewa lallai tana da halin da za ta attaro sakamakon zaɓe daga sassan ƙasa baki ɗaya ta hanyar amfani da fasahar zamani. Tun farko, sai da 'yan majalisun tarayya suka tafka zazzafar muhawara kan wannan…
Read More