26
Feb
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Hukumar Zaɓe na Ƙasa INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya ayyana buɗe zauren karɓar sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa na 2023 a hukumance. Shugaban na INEC ya ce za a fara tattara sakamakon ne daga gundumomi zuwa ƙananan hukumomi, daga nan sai a kai matakin jiha. Ya ce bayan nan ne kuma za a kai sakamakon zuwa Abuja, babban birnin tarayya, a zauren tattara sakamakon. Yakubu ya ce baturen zaɓe idan ya zo sanar da sakamakon zaven jihar da ya zo da ita, zai faɗi ta yadda kowa zai ji, inda zai faɗi yawan mutanen…
