Month: April 2021

Hajjin 2021: Jihar Kano ta ƙaddamar da shirin yi wa maniyyata rigakafin korona

Hajjin 2021: Jihar Kano ta ƙaddamar da shirin yi wa maniyyata rigakafin korona

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Kula da Walwalar Alhazai ta Jihar Kano, ta ce ta ƙaddamar da shirin allurar rigakafin cutar korona ga maniyyatan Hajjin 2021 a jihar inda ta soma bada allurar ta kan ma'aikatanta. A wata sanarwa da ta fitar ta hannun jami'arta ta hulda da jama'a, Hadiza Abbas Sunusi, hukumar ta ce ta soma gudanar da shirin ne a Larabar da ta gabata inda aka buɗe fagen yin allurar da fara yi wa Sakataren Hukumar, Muhammad Abba Dambatta. A cewar Sakataren, an ƙaddamar da shirin yin allurar ne domin cika sharaɗin da Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta…
Read More
Filato: An tsige DPO bisa zargin kashe wasu makiyaya biyu

Filato: An tsige DPO bisa zargin kashe wasu makiyaya biyu

Daga BASHIR ISAH Kwamishinan 'Yan Sanda na Jihar Filato, Edward Egbuka, ya tsige tare da tsare DPO mai kula da yankin ƙaramar hukumar Bassa a jihar, wato DSP Solomon Machu, bisa zargin kisan wasu makiyaya biyu a jihar. An zargi DPOn ne da kashe Musa Giwa ɗan shekara 24, da Ibrahim Sa'idu ɗan shekara 30, ta hanyar mafani da bindigabayan da 'yan bijilanti na yankin suka kama makiyayan a ƙauyen Dogon Daji tare da miƙa su ga DPOn cikin ƙoshin lafiya a Lahadin da ta gabata. Manhaja ta tattaro cewa a Alhamis da ta gabata 'yan sanda suka miƙa gawarwakin…
Read More
Duk littafin da na rubuta ba ƙagaggen labari ba ne ya faru da gaske – Fatima Ibrahim Garba Ɗanborno

Duk littafin da na rubuta ba ƙagaggen labari ba ne ya faru da gaske – Fatima Ibrahim Garba Ɗanborno

*Zaluncin 'yan kasuwa ne ya durƙusar da marubutan mu - Fatima DAGA AISHA ASAS Fatima Garba Ɗanborno ba za a kira ta ɓoyayya ba musamman a wajen ma'abota karance-karancen littafan Hausa, domin ta yi fice wajen fitar da littattafai masu tarin faɗakarwa gami da ilimintarwa da kuma nuni cikin nishaɗi. Shi ya sa a wannan makon Jaridar Manhaja ta zagaya don zaƙulo wa masu karatu ita don jin wace ce ita? Me ya kai ta ga fara rubutu da shiga harkokin marubuta tsundum? Tare kuma da jin irin nasarori da faɗi-tashin da ta yi kafin ta zama cikakkiyar marubuciya? Duk…
Read More
An ceto baƙin haure 483 a gaɓar tekun Libya, inji IOM

An ceto baƙin haure 483 a gaɓar tekun Libya, inji IOM

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Kula da Sha'anin 'Yan Gudun Hijira ta Ƙasa da Ƙasa ta Majalisar Ɗinkin Duniya (IOM), ta ce baƙin haure 483 aka ceto daga gaɓar tekun Libya a yammacin ƙasar. Hukumar ta ce dogarawan tsaron tekun Libya sun yi aikin ceton baƙin ne a lokuta daban-daban. IOM na mai cewa duk da dai an bai wa baƙin taimakon gaggawa da sauran kulawar da ta dace, sai dai ta ce tashar ruwan Libya ba ta da tsaro. Ta ci gaba da cewa baƙin haure sama da 4,500 ne aka daƙile ko aka cece su a wannan shekara…
Read More
Duk namijin ƙwarai ba zai zauna da macen da za ta iya kisa ba – Khadija S. Mohammed

Duk namijin ƙwarai ba zai zauna da macen da za ta iya kisa ba – Khadija S. Mohammed

DAGA AISHA ASAS Wannan makon mun yi wa ma su karatun jaridarmu babban kamu a wannan shafin, domin mun samu damar tattaunawa da matar nan da ke bai wa ma'aurata da masu shirin yin aure shawarwari domin inganta zaman aurensu, har ta kai su kasance takalmin kaza. Da yake irin wannan cibiya ta Khadija Sa'ad Mohammed tamkar baƙon abu ne ga mutanen Arewacin Nijeriya, amma idan masu karatu suka biyo mu za su ji yadda baƙuwar tamu suke samun koke da jin matsalolin zamantakewar aure da kuma yadda suke bada shawara kuma a samu mafita da daidaito. Ga dai yadda…
Read More
Ogun: Gwamna Abiodun ya ƙaddamar da Amotekun

Ogun: Gwamna Abiodun ya ƙaddamar da Amotekun

Daga WAKILINMU A matsayin wani mataki na ci gaba da yaƙi da matsalar tsaro a Jihar Ogun, Gwamnan jihar, Dapo Abiodun, ya ƙaddamar da shirin bada tsaro na cikin gida, wato Amotekun. Da yake jawabi yayin ƙaddamawar, Gwaman ya ce ba a samar da Amotekun don ta zama kishiya ga sauran hukumomin tsaro ba, face don ƙarfafa wa fannin tsaron jihar. Ya ce gwamnatinsa za ta bai wa shirin Amotekun cikakken haɗin kai tare da samar masa da kayan aikin da yake buƙata don cim ma manufar kafa shi. Tuni Gwamnan ya nuna alamar mara wa shirin baya ta hanyar…
Read More
Rundunar JBPT ta kama haramtattun kayayyaki na N61

Rundunar JBPT ta kama haramtattun kayayyaki na N61

Daga AISHA ASAS A ci gaba da yaƙi da harkar fasa-ƙwauri da take yi a sassan ƙasa, Rundunar Haɗin Gwiwa ta Joint Border Patrol Team (JBPT) rukuni na 3 a jihar Kwara, a cikin makonni 3 ta fatattaki 'yan fasa-ƙwauri tare da ƙwace tarin kayayyaki wanda a ƙiyasce kuɗinsu ya kai Naira milyan N61. Kazalika, randunar ta samu nasarar daƙile wasu baƙin haure masu shiga ƙasa ba a bisa tsarin da doka ta shimfiɗa ba. Daga cikin tarin kayayyakin da rundunar ta kama, har da shinkafar ƙetare buhu 1,274, motoci tokumbo guda 23, ƙaramar bindiga ƙirar gida da alburusai guda…
Read More